No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar Majalisar Ɗinkin Duniya mai kula da ‘yan gudun hijirar Falasɗinawa, (UNRWA) ta bayyana cikin baƙin ciki cewa ma’aikatanta 64 ne suka rasa rayukansu a Gaza a rikicin Isra’ila da Hamas.

Hukumar ta ƙara da cewa wani abin takaicin shi ne, ɗaya daga cikin ma’aikatan da aka kashe harda ɗaukacin iyalinsa da suka haɗa da ‘ya’ya takwas da matarsa ​​yayin da suke gida.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Mai magana da yawun hukumar, Juliette Touma, ta bayyana damuwa game da cunkoso a matsuguni 450 da suke gudanarwa a faɗin Gaza, inda jimillar mutane 670,000 suka nemi mafaka.

Lamarin dai ya yi ƙamari, inda rahotanni ke cewa cututtuka kamar su zawo da gudawa suna yaɗuwa.

Ana buƙatar tsagaita wuta na jin ƙai cikin gaggawa saboda hatta wuraren da ya kamata a kiyaye, da suka haɗa da majami’u da masallatai da wuraren Majalisar Ɗinkin Duniya, abin ya shafa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...