Connect with us

Labarai

Muna so gwamnati ta fara biyan mu albashi – masu gadin maƙabartu a Yobe

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Masu kula ko kuma masu gadin maƙabartu a jihar Yobe, sun yi ƙira ga gwamnatin jihar Yobe, da ta taimaka ta fara biyansu albashi. Sun yi wannan ƙiran ne a lokacin da Neptune Hausa ta ziyarci wasu daga cikin maƙabartun a garin Potiskum, domin ganin irin yadda ruwa ya mamaye wasu maƙabartun, wanda hakan ya yi sanadiyyar rubzawar ƙabarurruka da yawa a daminar da ta gabata.

Neptune Hausa ta zanta da Malam Adamu Yawale, ɗaya daga cikin masu gadin maƙabartar bayan Asibitin ƙwararru da ke Potiskum (Yobe State Specialist Hospital, Potiskum). Ya shaida wa wakilinmu cewa “A wannan maƙabarta, muna fama da matsaloli, musamman na rubzawar ƙaburbura, kuma babu ƙasar cuko. Muna so gwamnati ko wasu al’umma su taimaka su kawo mana ƙasa don mu cike ƙaburburan da suka rubza.

Sannan muna tsananin buƙatar itace na buso a wannan maƙabarta. Lokuta da dama sai an kawo za a binne mutum, amma babu itacen da za a saka kabari wanda za a binne mutum da shi. Dole sai dai ‘yan’uwan mamacin su fita su je su sayo itacen, kafin a binne mutum”.

KU KUMA KARANTA: Tinubu ya ba da umarnin biyan malaman jami’a albashin watannin da suka yi suna yajin aiki

Malam Adamu, ya ƙara da cewa “kullum a wannan maƙabarta muke wuni. Mune muke kula da ita, mune muke tona ƙaburburan da ake zuwa ake binne bayin Allah. Ba ma samun abin kashewa, da na cefane ga iyalanmu, sai dai idan an kawo jana’iza, idan jama’a sun taimaka mana da sadaka, sannan muke samun ɗan wani abu”.

Malam Sulaiman Sa’id, ɗaya ne daga cikin masu gadin maƙabartar Mamman B. Ali, wadda aka fi sani da maƙanartar MAL. Ya shaida wa wakilinmu cewa “wannan maƙabarta, ta fi kowace maƙabarta girma a garin Potiskum. Amma duk girmanta wannan maƙabarta, ba ta da hanyar ruwa, ka ga kuwa idan wuri ya yi girma kuma babu hanyar ruwa, to dole ne wurin ya nashe. Ta haka yake samun dama ya je ya shiga kabarurruka, ya rubzasu. Duk kyan aikinku a wannan maƙabarta, sakamakon rashin hanyar ruwa, sai ruwan ya je ya rusa kabarurruka.

Babban abin da muke buƙata shi ne gwamnati ta zo ta cire mana hanyar ruwa guda biyu ko uku, wanda ruwan zai samu hanyar fita waje. Sannan muna tsananin buƙatar itace a wannan maƙabarta. Kusan dukkan ƙauyukan kusa damu, nan maƙabartar suke kawo jana’iza. Ana kawo jana’iza 20 zuwa 30 a kullum a wannan maƙabarta. To wannan ne yake sa wa duk yawan itacen da aka kawo wannan maƙabarta yake yawan ƙarewa. Babu shakka jama’a suna taimaka wa da itace, amma yawan jana’iza da ake kawo wa, shi ne yake kawo ƙarewar itacen da wuri.

Sannan buƙata ta gaba shi ne, muna so gwamnati ta fara biyanmu albashi. A iya sanina, a dukkan maƙabartu na garin Potiskum, waɗanda gwamnati take iya biyansu albashi, mutane biyu ne. Gwamnati ba ta biyan mutanenmu masu kula da dukkan maƙabartu kuɗi don su dinga ciyar da iyalansu. Muna so gwamnati ta dube mu da idon rahama, ta dinga biyanmu albashi, don mu dinga samun abin da za mu ciyar da iyalanmu”. inji shi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Published

on

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Afirka ta Yamma mai rarrabuwan kai ta gudanar da tarukan ƙolin shugabannin ƙasa guda biyu a ƙasashe daban-daban biyu a ƙarshen makon, inda aka gudanar da taro farko ranar Asabar a Nijar tsakanin shugabannin mulkin soja na yankin Sahel.
A gefe guda kuma za a gudanar da wani taron ƙoli ranar Lahadi a Najeriya inda shugabannin sauran ƙasashe mambobin ƙungiyar tattalin arziƙin yankin ta ECOWAS za su hallara.

Taron ƙolin da ake yi yau Asabar a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar, zai kasance karo na farko tsakanin shugabannin sojojin sabuwar ƙungiyar haɗin kan yankin Sahel wato Alliance of Sahel States ko kuma AES.

Mali, Burkina Faso da Nijar su ne suka kafa yarjejeniyar kare juna a watan Satumba, waɗanda suka bar babbar ƙungiyar ECOWAS a cikin watan Janairu.

Ficewar su daga ECOWAS, wani ɓangaren ya samo asali ne daga zargin da suke yi cewa Paris tana yiwa ƙungiyar katsalandan kana ba ta ba da taimakon da ya kamata a yaƙi da masu iƙirarin yaƙin jihadi.

Ficewar ta sa ƙasashen uku sun janye kansu daga Faransa da ta yi musu mulkin mallaka, suka kori sojojin Faransa masu yaƙi da masu iƙirarin jihadin kana suka juya zuwa ga ƙasashen da suke ƙira da aminan gaskiya, da suka haɗa da Rasha da Turkiya da kuma Iran.

KU KUMA KARANTA:Shugabannin Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa ƙungiyar haɗaka

Idan aka yi la’akari da munanan tashe-tashen hankula na ‘yan jihadi da ƙasashen uku ke fuskanta, “yaƙin da ta’addanci” da “ƙarfafa haɗin gwiwa” za su kasance kan ajandar taron ƙolin na yau Asabar, a cewar fadar shugaban ƙasar Burkina Faso.

Taron ƙolin da za a gudanar ranar Lahadi a Abuja zai ba shugabanni a ƙasashen ECOWAS damar tattaunawa a kan irin alaƙa da za su ƙulla da ƙungiyar ta AES.

Bayan wasu tarurrukan da suke yi tsakanin ƙasashe biyu, shugabannin uku na yankin Sahel sun yi taro a karon farko tun bayan da suka hau karagar mulki ta hanyar juyin mulki tsakanin shekarar 2020 zuwa 2023.

Continue Reading

Labarai

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Published

on

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

 

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewar ‘yan Najeriya miliyan 82, kimanin kashi 64 na ‘yan ƙasar ka iya fuskantar matsalar yunwa nan da shekarar 2030.

Haka kuma MƊD ta yi ƙira da gwamnatin ƙasar ta magance matsalar sauyin yanayi da matsalar ƙwari da sauran abubuwan da yi wa harkar noma barazana.

Jaridun Najeriya sun ambato jami’in Majalisar Ɗinkin Duniyar, Taofiq Braimoh – wanda ya wakilci kodinetan ayyukan jin ƙai na hukumar abinci da ayyukan noma na majalisar na bayyana haka lokacin da yake jawabi kan matsalolin ƙarancin abinci a taron ƙaddamar da shirin bunƙasa ayyukan noma na ‘CropWatch’ a birnin Abuja.

KU KUMA KARANTA:Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi maraba da sakin yara 21 da aka yi garkuwa da su

Mista Braimoh ya ce akwai buƙatar gwamnatin Najeriya ta ɗauki matakan da suka dace cikin gaggawa don magance matsalar.

“Gwamnatin Najeriya tare da haɗin gwiwa masu ruwa da tsaki, sun gudanar da bincike na shekara-shekara da suka saba gudanarwa kan abinci. Sakamakon binciken ya tayar da hankali, kimanin mutum miliyan 82 ne za su fuskanci yunwa nan da 2030,” kamar yadda Jaridun ƙasar suka ambato Braimoh na bayyanawa.

Ya ci gaba da cewa matsalar rashin abinci da ƙasar ke fama da shi, baya rasa nasaba da matsalar sauyin yanayi da duniya ke fama da ita, da matsalar ƙwari da wasu abubuwa da ke yi wa harkar noma barazana a ƙasar.

Hasashen na Majalisar Ɗinkin Duniyar na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsadar abinci, lamarin da ya tilasta wa gidaje da dama haƙura da sayen abincin da suka saba ci.

A cikin rahotonta baya-bayan nan, hukumar ƙididdigar ƙasar ta ce farashin abinci a ƙasar ya ƙaru zuwa kashi 40.66 a watan Mayu, matakin da aka jima ba a ga irinsa ba.

Continue Reading

Labarai

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Published

on

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta maka jaridar Daily Trust a kotu, tare da shigar da ƙorafi game da ita, a gaban ƙungiyar masu gidajen jarida ta Najeriya saboda abin da ta ƙira ”yaɗa kalaman neman tayar da rikici da karya aikin jarida”

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tana sane da yadda a cikin ‘yan watannin baya, jaridar Daily Trust ke yaɗa labaran da ke neman gogawa gwamnatin kashin kaji.

Da ya ke magana a wajen wani taron manema labarai a ranar Asabar, ministan yaɗa labaran ya kafa hujja da labaran da jaridar Daily Trust ta wallafa a game juyin mulkin Nijar, da wanda ya ce jaridar ta rubuta a kan shirin sauya sunan titin Murtala Muhammad da ke Abuja zuwa Wole Soyinka da kuma na baya bayan nan a game da sanya hannu a kan yarjejeniyar da ta shafi amincewa da auren jinsi.

KU KUMA KARANTA: Alaƙar soyayya tsakanin jinsi ɗaya ta haramta a Iraƙi

Ya yi bayanin cewa a dukkan labaran, gwamnatin ta gano yadda jaridar ta bayar da rahoto ba tare da gabatar da hujja ko shaidun zargin da ta yi ba, lamarin da kuma gwamnatin ke kallo a matsayin wani yunƙuri na wallafa ƙarya domin tunzura jama’a.

Ya ce: ‘’Ba mu taɓa tunanin Daily Trust da mutanen da ke da ita za su kai wannan mataki ba wajen neman tayar da rikici a ƙasar nan, ta hanyar zargin cewa gwamnati ta sanya hannu a kan yarjejeniyar tallata auren jinsi. Wannan tsabar zalunci ne saboda babu wannan tanadi a cikin yarjejeniyar.’’

Ministan ya koka da yadda wannan labarin ya janyo huɗuba mai zafi daga wasu malaman addini da kuma jefa jama’a cikin halin ɗarɗar, wanda kuma ya ce jaridar ce ta janyo.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

Saboda haka, ministan ya ce ‘’Gwamnatin tarayya za ta bi duk hanyoyin da doka ta amince da su, domin neman haƙƙi a kotu.’’

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like