No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wasu ‘yan bindiga da dama sun kai hari fadar Sarkin Maru Abubakar Gado Maigari inda suka kashe wani mai gadin fadar a daren Laraba.

‘Yan bindigan sun sake komawa fadar a daren Alhamis da nufin kashe ko kuma sace sarkin, amma suka kai farmaki kan jama’ar da ba su ji ba, ba su gani ba lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane huɗu.

Sarkin da ƙyar ya tsallake rijiya da baya a harin da ‘yan bindigan suka kai a ranar Laraba da Alhamis da daddare, in ji wata majiya.

An tattaro cewa ‘yan ta’addan sun yi yunƙurin yin garkuwa da Sarkin bai yi nasara ba, inda suka riƙa kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba a lokacin da suka je gida gida suna neman mazauna garin da nufin yin garkuwa da su.

KU KUMA KARANTA: Mummunan harin da sojojin suka kai a Sakkwato, ya kawo ƙarshen ‘yan ta’adda da dama a jihar

Harsashin bindiga da dama ya janyo hasarar ababen hawa da wasu kayayyaki masu daraja, sannan kuma an jikkata wasu mutanen yankin da ba a san adadinsu ba a yayin aikin.

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal a wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai Munnir Haidara ya sanyawa hannu ya yi Allah wadai da harin tare da bayyana shi a matsayin dabbanci da rashin mutuntaka.

Gwamnan ya kuma bayar da umarnin rufe kasuwar Maru, ba tare da ɓata lokaci ba, har sai an daidaita matsalar tsaro a ƙaramar hukumar.

Manufar ita ce a wargaza duk wani shiri na ta’addanci na kai wa mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba a kasuwa hari, tare da samar da ƙarin na’urori da za su taimaka wa gwamnati da hukumomin tsaro wajen yaƙar masu aikata laifuka.

A farkon shekarar nan ne aka kai hari a hedikwatar ‘yan sanda da ke ƙaramar hukumar Maru, kuma an kashe wani DPO da wasu jami’ai a wani shingen bincike na ‘yan sanda.

An yi jana’izar waɗanda ‘yan bindiga suka kashe a ranar Juma’a da rana a ƙaramar hukumar Maru.

Har yanzu dai hukumomin ‘yan sanda a Zamfara ba su ce uffan ba kan lamarin.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...