No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar sojojin Najeriya ta bayyana cewa wani ƙasurgumin kwamandan ƙungiyar ta’addanci na Boko Haram, mai suna Bulama Bukar, ya miƙa wuya ga dakarunta a yankin Gubio, jihar Borno.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da darakta labarai na rundunar soji, Birgediya Janar Onyema Nwachukwu, ya saki a ranar Laraba, 18 ga watan Oktoba, a Abuja.

Jaridar Daily Nigerian ta rawaito cewa ɗan ta’addan da ya miƙa wuya ya kasance kwamandan sansanin Boko Haram a Tapkin Chad da ke ƙauyen Gilima a ƙaramar hukumar Abadam ta jihar Borno.

Ya ƙara da cewar, kayayyakin da aka samo daga ɗan ta’addan da ya miƙa wuya sun haɗa da bindigar AK 47 guda ɗaya, makamai 5, harsasai 7.62 guda 44, wuƙa ɗaya, babur ɗaya da kuɗi Naira 23,500.

“A yanzu haka, ana ɗaukar bayanan ɗan ta’addan.”

A halin da ake ciki, kakakin rundunar sojin ya ce dakarun soji na nan suna aikin buɗe wuta domin raba ƙasar da tsagerun ‘yan ta’adda, masu tayar da ƙayar baya da sauran miyagu a faɗin ƙasar.

KU KUMA KARANTA: Rashin tsugunar da ‘yan Boko Haram da suka miƙa wuya babban haɗari ne- Barista Bulama Bukarti

Mista Nwachukwu ya ce a kan haka ne dakarun bataliya ta 2 suka kai kwantan ɓauna kan wasu ‘yan ta’adda a yankin Udawa dake ƙaramar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna a ranar 17 ga watan Oktoba sannan suka sheƙe ‘yan ta’adda uku.

Ya ce wutan da aka buɗe masu ya sa sauran sun tsere, yayin da sojojin suka ƙwato wata bindiga ɗauke da harsashi 111, babura biyu, babban rediyon sadarwa mai ƙarfin gaske da kuma wayoyi guda biyu.

A cewarsa, wani soja ya rasa ransa a yayin arangamar, rahoton Leadership.

Ya ƙara da cewar a wannan ranar, dakarun Birgediya ta 1 sun kama wani da ake zargin yana kai alburusai a ƙaramar hukumar Birnin Magaji da ke jihar Zamfara.

Ya ce binciken farko da aka yi ya nuna cewa wanda ake zargin yana hanyar kai wa wani shugaban ‘yan bindiga mai suna Gishiri harsashi ne.

A cewarsa, dakarun ‘yan banga sun ƙwato wata jaka ɗauke da harsashin 7.62mm guda 224, wayar hannu ɗaya da kuma kuɗi naira 4,000 daga hannunsa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...