No menu items!

Sample Page Title

Date:

Iran ta gargaɗi Isra’ila da cewa za ta iya kai harin riga-kafi cikin ‘yan sa’o’i masu zuwa’  idan har Isra’ila ta ci gaba da kai hare-hare kan Hamas a Gaza.

Tun bayan da ƙungiyar Hamas ta ƙaddamar da harin ba-zata kan Isra’ila a ranar 8 ga watan Oktoba, inda ta kashe fararen hula fiye da dubu ɗaya tare da yin garkuwa da ɗaruruwan ‘yan Isra’ila, Isra’ila ta mayar da martani, inda ta kai hare-hare kan maɓoyar Hamas da ke Gaza tare da daƙile mai, abinci da ruwa, a daidai lokacin da Isra’ila ke shirin mamaye Gaza.

Iran a ranar Talata, 17 ga Oktoba ta yi gargaɗin cewa wakilan ƙasar da ke yammacin Asiya za su iya kai hare-hare kan Isra’ila “a cikin sa’o’i masu zuwa”.

Haka nan kuma yayin da yake ishara da ganawar da ya yi da babban sakataren ƙungiyar Hizbullah Hassan Nasrallah a baya-bayan nan, ministan harkokin wajen ƙasar Iran Hossein Amirabdollahian ya bayyana cewa: A cikin sa’o’i masu zuwa, duk wani mataki na turjiya kan gwamnatin sahyoniyawa abu ne mai yiwuwa.

KU KUMA KARANTA: Yaƙin Falasɗinawa da Isra’ila: An fara kwaso ’yan Najeriya da suke can

Shugabannin gwagwarmaya ba za su ƙyale gwamnatin sahyoniyawan ta yi duk abin da ta ga dama a Gaza ba, sannan ta koma wasu fagagen gwagwarmayar,” in ji Amirabdollahian.

Ministan na Iran ya ƙara da cewa ƙasarsa ba ta ba da umarni ba ga ƙungiyoyin da Iran ke marawa baya a duk faɗin yankin amma tana goyon bayansu.

Amirabdollahian ya kuma yi barazanar idan yaƙin ya faɗaɗa zuwa wasu fagagen, “zai canza taswirar Isra’ila.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...