No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Ɗinkin Duniya a Falasɗinu ta ce a yanzu ruwa ya zama “al’amari na rayuwa da mutuwa” ga mutanen yankin Zirin Gaza bayan da Isra’ila ta katse ruwan da suke samarwa.

Hukumar ba da agaji ta Majalisar Ɗinkin Duniya da ke kula da ‘yan gudun hijirar Falasɗinu a yankin Gabas ta Tsakiya (UNRWA) ta faɗa a ranar Asabar cewa sama da mutane miliyan biyu ne ke cikin haɗari sakamakon ƙarewar ruwa.

“Ya zama batun rayuwa da mutuwa.  Ya zama dole, ana buƙatar isar da man fetur a Gaza a yanzu domin samar da ruwa ga mutane miliyan biyu,” in ji Kwamishinan UNRWA Janar Philippe Lazzarini.

KU KUMA KARANTA: Rikicin Gaza: Netanyahu na neman tayar da yaƙin duniya na uku

Ba a ba da izinin shigar da kayan agaji zuwa Gaza tsawon mako guda ba, a cewar hukumar.

Ruwa mai tsafta ya ƙare a Zirin Gaza yayin da tashar ruwan cibiyoyin ruwan jama’a suka daina aiki.  A yanzu dai an tilastawa Falasɗinawa amfani da gurɓataccen ruwa daga rijiyoyi, lamarin da ke ƙara barazanar kamuwa da cututtuka.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...