No menu items!

Sample Page Title

Date:

Najeriya ta kwaso ’yan ƙasarta sama da 300 da suka maƙale a yayin da ake ci gaba da gwabza faɗa tsakanin Isra’ila da mayaƙan Falasɗinawa.

Najeriya ta kwashe su ne bayan da suka tsallaka zuwa ƙasar Jordan, daga Isra’ila inda suka kai ziyarar ibada daga Jihar Legas.

Ga yadda gwamnatoci ke kwashe ’yan ƙasashensu daga Isra’ila da yankin Falasɗinawa.

An kwashe ’yan Najeriyar masu ziyarar ibada a Isra’ila ne a yayin da dubban ’yan ƙasashen waje suka maƙale a Isra’ila da Falasɗinu sakamakon yaƙin ɓangarorin da ya shiga kwana da biyar.

Aƙalla mutum dubu uku ne suka rasu, wasu kimanin dubu huɗu suka jikkata daga ɓangarorin biyu, lamarin da ya sa ƙasashe rububin kwashe ’yan ƙasashen da ke can zuwa gida.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...