No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin Amurka ta sanar da janye tallafin Dala miliyan 442 da take ba wa Jamhuriyar Nijar, bayan yunƙurinta na dawo da Bazoum ya gagara

Amurka ta sanar da hakan bayan da ta ayyana ƙwace mulkin da sojojin ƙasar suka yi a watan Yuli a matsayin juyin mulki.

Wani babban jami’in Amurka ya ce, ƙasarsa ta “ɗauki matakin ne saboda a tsawon wata biyu da suka gabata mun bi duk hanyoyin da suka kamata domin dawo da halastacciyar gwamnati a Nijar amma abin ya gagara.”

KU KUMA KARANTA: Rundunar sojin Faransa za ta fara kwashe dakarunta daga a jamhuriyar Nijar

Hakan na zuwa ne a ranar da rukuni na biyu na sojojin Faransa suka fice daga Nijar, tun bayan juyin mulkin da sojoji ƙarƙashin Janar Abdourahmane Tchiani suka yi wa Shugaba Mohamed Bazoum.

Amurka da Faransa sun kafa sansanonin soji domin taimakawa wajen yaƙar ta’addanci a Nijar a zamanin Bazoum, wanda sojojin ke zargin sa da kasancewa dan amshin shatan Faransa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...