No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnan jahar Kano ya aikewa da majalisar jahar Kano ɗan ƙwarya-ƙwaryar kasafin kuɗi kimanin sama da naira biliyan 58.

Rahotanni sun ce kasafin Kuɗin ya ƙunshi gina gadar Sama da ta ƙasa a sha-tale -talen Titin Ƙofar Ɗan’agundi da Tal’udu, don rage cunkosan ababen hawa, anyi la’akari da tituna ne da ke da alaƙa da yawancin manyan makarantun gaba da sakandire a jahar Kano.

Haka kuma kasafin yana ƙunshe da harkar ilimi, wanda ke da kaso mafi tsoka a cikinsa, gyaran makarantun sakandire da ɗaukar nauyin ‘ya’yan jahar Kano zuwa karatu ƙasashen waje, wato digiri na biyu (Msc).

A harkar lafiya kuma, abubuwan da suka haɗa da gyare-gyaren Asibitoci dama sanya na’urorin aiki na zamani, haihuwa kyauta da ba da magani kyauta,, da sauran buƙatu na ɓangaren lafiya.

KU KUMA KARANTA: Kotu ta umarci gwamnatin Kano ta biya diyyar rushe-rushen shagunan ‘yan kasuwa a jihar

Ɓangaren Auren Zawarawa! Don ragewa Al’umma raɗaɗi da cika musu burukan su na aiwatar da sunnar Annabinmu tsira (S.A.W). Da sauran manyan Ayyukan rayar da Al’umma.

Shugaban kwamitin tsare-tsare na majalisar jahar Kano ne ya bayyana hakan bayan zaman majalisar na ranar juma’a.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...