No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumomin Indiya sun kama sama da mutane dubu ɗaya a arewa maso gabashin ƙasar a ranar Talata a wani ɓangare na yaƙi da aurar da ƙananan yara a yankin a bana.

Tuni dai jihar Assam ta kame mutane 4,000 a wani yunƙuri da ta yi a watan Fabrairu, ciki har da iyayen yaran da suka yi aure da kuma ma’aikatan gwamnati waɗanda suka yi rajistar auren ƙananan yara.

Alƙaluman da Majalisar Ɗinkin Duniya ta fitar sun nuna cewa akwai ƙananan yara sama da miliyan 220 da suka yi aure a Indiya.

Duk da cewa al’amuran auren ƙanana yara sun ragu matuƙa a wannan ƙarnin, har yanzu al’adar tana yaɗuwa.

KU KUMA KARANTA: Kotu ta raba auren wata 10 ta hanyar “Khul’i”

A cewar Asusun Tallafa wa Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF), kalmar auren yara tana nufin duk wani aure ko kuma wani tsarin zama tsakanin yaro da bai kai shekara 18 da wani babba ko yaro.

Babban Ministan Jihar Himanta Biswa Sarma ya sanar da cewa, ‘yan sanda sun ƙaddamar da wani samame na musamman wanda aka fara tun da sanyin safiya.

Ya wallafa a dandalin sada zumunta na X (wanda aka fi sani da Twitter): cewa “Yawancin adadin waɗanda ake tsare da su zai iya ƙaruwa,” wanda a halin yanzu adadin ya kai 1,039.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...