Sojojin saman Najeriya sun dagargaza maɓoyar ‘yan ta’adda da suka addabi arewa maso gabas

0
227

Rahoton jaridar ‘The Nation’ na cewa hare-haren da jiragen yaƙin sojojin saman Najeriya (NAF) suka kai sun kashe ‘yan ta’adda da dama da ke yin sintiri a yankin tafkin Chadi na jihar Borno.

Harin na sama ya kuma lalata maɓoyar ‘yan ta’addar, da gine-gine, da kuma  maɓoyarsu.

Kakakin NAF, Air Commodore Edward Gabkwet, ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Litinin, 2 ga Oktoba.

Ya ce an far wa ‘yan ta’addan ne a wuraren da suke Tumbun Fulani da yankin Tumbun Shitu da ke gaɓar tafkin Chadi daga ranar 27 zuwa 30 ga watan Satumba.

KU KUMA KARANTA: Hukumar EFCC ta kama maɓoyar ‘Yahoo-Yahoo’ a Benuwe, ta kama mutane 14 da ake zargi

Kakakin NAF ya ce hare-haren ta sama ya zama wajibi ne bayan da sojoji suka tabbatar da ayyukan ‘yan ta’addan “ya zama barazana ga tsarin soja da ‘yan Najeriya masu bin doka da oda da ke zaune a wuraren.”

Gabkwet ya ce: “A Tumbun Fulani, an ga ‘yan ta’adda suna loda jarkoki a cikin manyan motoci biyu da aka ɓoye a ƙarƙashin bishiyoyi.

Leave a Reply