Mutane shida a Kaduna sun mutu sakamakon harin ‘yan bindiga

0
246

Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane shida a wani sabon hari da suka kai a ƙauyen Takanai da ke ƙaramar hukumar Zango Kataf a jihar Kaduna.

Rahotanni sun ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 7 na dare, ranar Talata. Wani mazaunin unguwar Samson Markus, wanda ya tabbatar wa manema labarai harin a ranar Laraba, ya ce lamarin ya faru “lokacin da ba a yi tsammani ba”.

A cewarsa, waɗanda abin ya shafa sun haɗa da ƙananan yara biyu da kuma ‘yan gida ɗaya.

“ ‘Yan bindigan sun zo ne da misalin ƙarfe 7 na dare lokacin da ba mu yi tsammanin irin wannan abu na iya faruwa ba.

KU KUMA KARANTA: Harin makami mai linzami a Yukren ya kashe mutane 16

Muna cikin harkokinmu na yau da kullum, kwatsam sai muka ji ƙarar harbe-harbe.

“Kowa ya fara gudu don tsira. An kashe mutane huɗu daga iyali ɗaya da kuma wasu biyu daga gida ɗaya, ciki har da yara biyu,” in ji Mista Markus.

A cewarsa, ‘yan bindigar sun tsere daga yankin kafin isowar jami’an tsaro. Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ba ta ce uffan ba kan lamarin har ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Leave a Reply