No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane shida a wani sabon hari da suka kai a ƙauyen Takanai da ke ƙaramar hukumar Zango Kataf a jihar Kaduna.

Rahotanni sun ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 7 na dare, ranar Talata. Wani mazaunin unguwar Samson Markus, wanda ya tabbatar wa manema labarai harin a ranar Laraba, ya ce lamarin ya faru “lokacin da ba a yi tsammani ba”.

A cewarsa, waɗanda abin ya shafa sun haɗa da ƙananan yara biyu da kuma ‘yan gida ɗaya.

“ ‘Yan bindigan sun zo ne da misalin ƙarfe 7 na dare lokacin da ba mu yi tsammanin irin wannan abu na iya faruwa ba.

KU KUMA KARANTA: Harin makami mai linzami a Yukren ya kashe mutane 16

Muna cikin harkokinmu na yau da kullum, kwatsam sai muka ji ƙarar harbe-harbe.

“Kowa ya fara gudu don tsira. An kashe mutane huɗu daga iyali ɗaya da kuma wasu biyu daga gida ɗaya, ciki har da yara biyu,” in ji Mista Markus.

A cewarsa, ‘yan bindigar sun tsere daga yankin kafin isowar jami’an tsaro. Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ba ta ce uffan ba kan lamarin har ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...