An kama ɓarayin da suka fasa shago suka saci wayoyin hannu 996 da kwamfuta tara

0
280

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu mutane biyar da ake zargin ɓarayi ne tare da ƙwato wayoyin hannu guda 996 da aka sace, da kwamfutocin tafi da gidanka guda tara da katin ATM da dai sauransu.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Talata, 26 ga Satumba, 2023, ya ce ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin Ibrahim Adamu ya fasa shaguna goma sha ɗaya a Kasuwar GSM ta Ɗansulaika inda suka yi awon gaba da wayoyin hannu, teburi, kwamfutocin tafi da gidanka.  da wasu kuɗaɗen tallace-tallace.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda a Kano sun kama ɓarayi sama da dubu

Wata tawagar ‘yan sanda ta ƙaddamar da wani samame ƙarƙashin jagorancin jami’an leƙen asiri, inda ta kai ga cafke wanda ake zargin a unguwar Sallari da ke ƙaramar hukumar Tarauni a jihar.

Adamu ya amsa laifin aikata laifin ne shi kaɗai, sannan ya jagoranci jami’an tsaro wajen ƙwato kayayyakin da aka sace da suka haɗa da wayoyin hannu guda 106.

Leave a Reply