No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Ministan Abuja Nyesom Wike ya soke ikon mallakar filayen ɗan takarar shugaban Najeriya a jam’iyyar LP, Mista Peter Obi da na tsohon gwamnan Cross River Liyel Imoke da ke birnin tarayyar.

Cikin wata sanarwa da babban sakatare a ma’aikatar Abuja, Olusade Adesola ya fitar, ta nuna cewa filayen Peter Obi da na Imoke na daga cikin fuloti 165 da hukumomin babban birnin suka ƙwace.

Sanarwar ta ce Wike ya soke ikon mallakar filayen ne saboda rashin gina su da aka yi.

Sauran manyan mutanen da matakin soke mallakar filayen ya shafa, akwai tsohon ministan tsare-tsare na ƙasa, Udo Udoma da tsohon sakataren gwamnatin tarayya Ufot Ekaett, da tsohon sanatan Edo ta Arewa, Sanata Victor Oyofo.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...