Wane hali ake ciki dangane da wutar lantarki a Birnin Kebbi?

0
201

Bayanai daga majiya mai tushe dangane da lamarin wutan lantarkin garin Birnin kebbi da jihar Kebbi na cewa babu takamammen ƙa’idar ranar da za a mayar da wutar.

Sai dai Majiyarmu ta ƙara da cewa hukumomin da tafiyar da gyaran lamarin ya shafa suna aiki tuƙuru domin ganin an kammala aikin da ake yi don ganin an mayar wa jama’a wutar lantarki ba da jimawa ba.

KU KUMA KARANTA: Kamfanin wutar lantarki ta dawo da wuta a Sakkwato

Majiyar ta ce:
” TCN da KEDCO suna da Corporate Information Department, wanda ke da alhakin sanarwa tare da fitar da labarai dangane da irin wannan lamari. Matuƙar an daidaita lamurra wannan sashe zai fitar da sanarwar mataki da ake kai, kuma za a sanar da jama’a”.

Leave a Reply