Connect with us

Labarai

Gwamnan Osun ya tsallake rijiya da baya, yayin da jirgin da yake ciki ya kama da wuta

Published

on

Rahotanni sun bayyana cewa Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun da muƙarrabansa sun tsallake rijiya da baya a wani hatsarin jirgin sama bayan jirgin da suka shiga, ya kama wuta daf da tashinsa.

Wani rahoto da jaridar Leadership ta fitar, ya nuna cewa, a ranar Talata, 5 ga Satumba, 2023, wani Bombadier Global Express 6000, mallakin hamshaƙin attajirin ɗan kasuwa, Cif Adedeji Adeleke, ya kama wuta a tashar tashin jirgin sama na Murtala Mohammed International Airport (MMIA) a Legas.

Cif Adeleke shi ne mahaifin mawaƙi, David Adeleke, wanda aka fi sani da Davido, kuma ɗan uwa ne ga gwamnan jihar Osun, Ademola Adeleke.

KU KUMA KARANTA: Jirgin ƙasa ya tsallake rijiya da baya a hanyar Abuja zuwa Kaduna (Bidiyo)

Lamarin ya faru ne a sashin gida na filin jirgin da misalin ƙarfe tara na safe a daidai lokacin da jirgin ke shirin tashi daga Legas zuwa Abuja.

Rahoton ya bayyana cewa jirgin da Gwamna Adeleke da muƙarrabansa da ke cikin jirgin, an tuƙa shi ne zuwa ƙarshen titin jirgin daf da tashinsa, sai aka ji ƙarar fashewar wani abu daga injin jirgin.

Rahoton ya ƙara da cewa, kafin tashin jirgin, an ajiye jirgin ne a babban ma’aikatar sufurin jiragen sama na Executive Jet.

Sam Iwuajoku, babban jami’in gudanarwa (CEO), Executive Jets, waɗanda suka mallaki hangar da aka ajiye jirgin mai zaman kansa, ya bayyana cewa jirgin na Cif Adeleke ya samu Lalacewar Abun Wuta (FOD) wanda ya sa jirgin ya yi zafi sosai, wanda ya haifar da tashin hankali fashewar.

“Lokacin da aka tashi, injin yana da zafi sosai kuma ya faru ne sakamakon gijen tsuntsu a ɗaya daga cikin injinan jirgin. Ya faru ne lokacin da aka ajiye jirgin ba a rufe shi yadda ya kamata ba, tsuntsaye za su gina gida kuma duk abin da suka kawo cikin injin jirgin zai iya haifar da zafi mai tsanani” Sam Iwuajoku ya shaida wa jaridar.

Ya faru da ɗaya daga cikin jirgin sama na a 2021, dole ne muka cire injin kuma muka kai injin ƙasar Jamus tsawon watanni 14 ana gyaransa.  Don haka, abu ne gama gari a Afirka saboda muna da tsuntsaye a kusa, ”in ji shi.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like