No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Anambra ta sanar da rasuwar ɗaya daga cikin jami’anta ASP Anthony Ogbodo.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, DSP Ikenga Tochukwu, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Awka, a ranar Lahadi, ya ce jami’in ya rasu ne a wani mummunan hatsarin mota da ya rutsa da babur ɗinsa da wata motar safa a ranar Asabar, 16 ga Satumba, 2023.

A cewarsa, direban motar bas ɗin da ya kakkaɓo jami’in ya kai shi Asibiti da ke Enugwu Ukwu kafin ya rasu.

“An kama direban kuma an kai shi kurkuku yayin da ake gudanar da bincike kan musabbabin hatsarin.

KU KUMA KARANTA: Mutane 14 sun mutu, sakamakon hatsarin jirgin sama a Brazil

“Wannan shi ne don ƙaryata maganganun ɓatanci da ake yaɗawa a shafukan sada zumunta na alaƙanta mutuwar jami’in da dalilai daban-daban.

“Rundunar ‘yan sandan ta yi alhinin rasuwar jami’in tare da yin ta’aziyya ga iyalansa da masoyansa bisa wannan mummunan rashi da ya yi.

“Kwamishanan ‘yan sanda, CP Aderemi Adeoye ya ba da tabbacin cewa za a gaggauta yin adalci a shari’ar,” in ji Ikenga.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...