Connect with us

Labarai

‘Yan bindiga sun kashe fastoci 23, sun rufe coci sama da 200 a Kaduna – Ƙungiyar CAN

Published

on

Shugaban ƙungiyar Kiristocin Najeriya (CAN) reshen jihar Kaduna, Joseph Hayab, ya ce ‘yan bindiga sun kashe fastoci 23 tare da rufe coci sama da 200 a faɗin jihar Kaduna.

Mista Hayab ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ya yi da kwamishinan ‘yan sandan jihar, Musa Garba, da limaman coci-coci daban-daban na ƙananan hukumomi 23 na jihar.

Shugaban na CAN ya bayyana cewa cocin ya shiga mawuyacin hali sakamakon ayyukan masu aikata laifuka a jihar.

Ya ce: “Wani Fasto da aka yi garkuwa da shi a ranar 8 ga Agusta 2023, ya shaida wa shugabannin CAN cewa akwai Kiristoci sama da 215 da ‘yan bindigar suka sace a dajin Birnin Gwari.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga a Kebbi sun kashe mutane biyu, sun sace mutane bakwai

“Har yanzu suna nan kuma Fasto ya shaida mana cewa ‘yan bindigar sun nemi ya yi addu’a ga Kiristoci 215 a lokacin da yake cikin kogon su.

“Muna ƙira ga Kwamishinan ‘yan sanda, da ya duba wannan batu a tsakanin sauran mutane gaba ɗaya don ƙara ƙarfafa ƙwarin gwiwar jama’a,” in ji Mista Hayab.

Shima da yake jawabi, tsohon babban sakataren ƙungiyar Evangelical Church Winning All, (ECWA), a faɗin duniya, Yunusa Nmadu, da sauran limaman cocin da suka yi jawabi a wurin taron sun buƙaci kwamishinan ‘yan sandan ya kuma yi la’akari da kamo limamai da suka tsunduma cikin wa’azin ƙiyayya da kalaman ƙiyayya.

Limaman sun yi ƙira ga kwamishinan ‘yan sanda da ya duba lamarin masu sayar da miyagun ƙwayoyi, inda suka ce galibin laifukan ana aikata su ne ta hanyar amfani da miyagun ƙwayoyi.

Da yake mayar da martani, kwamishinan ‘yan sandan, ya jaddada cewa aikata laifuka ba shi da addini, yana mai cewa duk wanda ya aikata wani laifi to a ƙira shi a matsayin mai laifi ba tare da bayyana shi a matsayin Kirista ko Musulmi ba.

“Tsaro alhakin kowa ne ba na gwamnati kaɗai ba. Yayin da gwamnati ke kan gaba wajen kare rayuka da dukiyoyi, ana kuma sa ran ɗaiɗaikun mutane za su taka rawar gani musamman a fannin samar da bayanai.

“Taron ya kasance don ƙarfafa dangantakar da ke tsakanin ‘yan sanda da shugabannin addini da sauraron ƙalubalen da suke fuskanta tare da samar da hanyoyin da za a iya magance su.

“Rundunar ‘yan sanda ƙarƙashin jagorancina a jihar za ta yi iya ƙoƙarinta wajen gudanar da ayyukanmu. Ya kamata mu zama masu kiyaye ’yan’uwanmu.

“Koyaushe ku tuntuɓi jami’an tsaro da ke kewaye da al’ummomin ku da bayanan gaggawa da zarar kun gano mutanen da ake tuhuma,” kwamishinan ya umarci limaman.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: ‘Yan bindiga sun kashe mutane huɗu, sun sace 18 a Sakkwato | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like