Connect with us

Ƙasashen Waje

Mutane sama da dubu biyu ne suka mutu a Libya, sakamakon ambaliyar ruwan sama

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Yawan mutanen da suka mutu sanadin ambaliyar ruwa a ƙasar Libya ya ƙaru zuwa sama da 1,500 a birni guda ɗaya kawai, a cewar ministan da ya kai ziyara Derna, birnin gaɓar teku.

“Na kaɗu game da abin da na gani, tamkar ambaliyar tsunami,” Hisham Chkiouat, daga gwamnatin da ke sansani a gabashin ƙasar, ya ce.

Ruwa ya shafe mafi yawan sassan birnin Derna, wanda matsuguni ne ga mutane kimanin 100,000, bayan madatsun ruwa guda biyu da gadoji huɗu suka karye.

Sama da mutum 10,000 ne aka ba da rahoton cewa sun ɓata bayan gawurtacciyar guguwar da aka yi laƙabi Daniel ta auka, kamar yadda ƙungiyar ba da agaji ta Red Cross ta ba da rahoto.

KU KUMA KARANTA: Akwai barazanar ambaliyar ruwa a jihohi takwas a Najeriya – NEMA

Guguwar wadda ta auka wa ƙasar ranar Lahadi, ta kuma shafi biranen gabashin Libya, kamar Benghazi da Soussa da Al-Marj.

Hashem Chkiouat, ministan sufurin jiragen sama kuma ɗan kwamitin kai ɗauki na gwamnatin gabashin ƙasar ya faɗa wa BBC cewa karyewar ɗaya daga cikin madatsun ruwan da ke kudancin Derna, ya sa ruwa ya janye sassan birnin zuwa cikin teku.

Adadin mutanen da suka mutu gaba ɗaya, mai yiwuwa ne zai ƙaru fiye da haka.

“Ban zuzuta maganata ba, idan na cewa kashi ɗaya cikin huɗu na birnin ya ɓace. Gidaje da yawa, masu yawa nake faɗa muku, sun ruguje.”

Biranen gabashi irinsu, Benghazi da Sousse da kuma Al-Marj, su ma duk abin ya shafe su.

Tun da farko, Firaministan Osama Hamad ya faɗa wa wata tashar talbijin ɗin Libya cewa sun ƙiyasta mutane kimanin 2,000 ne suka mutu yayin da wasu dubbai kuma suka ɓace: “Unguwanni gaba ɗaya a birnin Derna sun ɓace, tare da mazaunansu… duka ruwa ya awon gaba da su.”

Tare da sauran yankunan gabashin ƙasar, birnin Misrata da ke yammacin Libya na cikin sassan da ambaliyar ruwan ta aukawa.

Ruwan sama ya haddasa mummunar ambaliya tare da zaftarewar ƙasa da kuma lalata gidaje da tituna da dama.

An ayyana yankin Derna a matsayin wanda mummunan bala’i ya aukawa, sannan an yi shelar zaman makoki na kwana uku.

Bayanai sun nuna cewa abu ne mai wuya a iya bayyana yawan mutanen da suka halaka, saboda babu hanyoyin sadarwa sosai.

Sannan kuma ga rashin tartibiyar gwamnati, sakamakon yaƙin da aka kwashe wajen shekara goma ana yi, tsakanin manyan abokan gaba biyu a ƙasar.

Sojojin ƙasar ta Libya bakwai ne aka bayar da rahoton sun ɓace a lokacin da suke gudanar da aikin agaji.

Jami’ai a gabashin ƙasar da ke ƙarƙashin ikon gwamnatin da ƙasashen duniya ba su amince da ita ba sun ayyana dokar hana fita, yayin da suka bayar da umarnin rufe makarantu da shaguna.

An sa dokar hana fita da kuma makoki na kwana uku a gabashin ƙasar

Masana sun yi gargaɗin cewa sauyin yanayi na duniya na nufin za a samu ƙaruwar tururi a lokacin bazara, wanda hakan zai haddasa mamakon ruwan sama da iska.

A yanzu mahaukaciyar guguwar mai tafe da mamakon ruwan saman ta isa yammacin Masar.

Ma’aikatar harkokin wajen Turkiyya ta ce za ta tura jiragen sama uku da za su kai ma’aikatan agaji da kuma kayan taimako zuwa ƙasar ta Libya.

Tun shekara ta 2014 Libya ke ƙarƙashin mulkin abokan gabar biyu bayan kashe daɗaɗɗen shugaban ƙasar Muammar Gaddafi a 2011.

Gwamnatin Firaminista Fayez al-Serra wadda ke samun goyon bayan majalisar ɗinkin duniya na yaƙi da tawayen Janar Khalifa Haftar wanda ƙasashe da hukumomin duniya ba su amince da mulkinsa ba kuma yake riƙe da iko a yankin gabashin ƙasar.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Abubuwan da ya kamata a sani game da sabuwar wayar iPhone 15 - LEGEND FM DAURA

  2. Pingback: Ana ci gaba da jimamin waɗanda suka mutu a ambaliyar ruwa a Libya | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like