No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wasu ‘yan bindiga da suka kai farmaƙi ƙauyen Kwarikwarasa da ke ƙaramar hukumar Maiyama a jihar Kebbi a ƙarshen makon da ya gabata, sun kashe mutane biyu tare da yin garkuwa da wasu mutanen ƙauyen su bakwai.

Jaridar Daily trust ta ruwaito cewa ‘yan bindigan sun mamaye al’ummar ne da sanyin safiyar ranar Asabar, 9 ga watan Satumba.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun kashe basarake sun ƙona gawarsa a Imo

Gwamna Nasiru Idris ya ziyarci al’umma inda ya tabbatar da cewa gwamnati ta tanadi matakan daƙile sake aukuwar lamarin.  Ya ce ya bai wa jami’an tsaro dukkan goyon baya da haɗin kan da ya kamata domin yaƙar miyagun ayyuka a faɗin jihar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...