No menu items!

Sample Page Title

Date:

A ranar Litinin ɗin nan ne wani jirgin ruwa ɗauke da fasinjoji ya kife a garin Gurin da ke wajen ƙaramar hukumar Fufore a jihar Adamawa.

A cewar wata majiya, waɗanda abin ya rutsa da su galibi mata ne da ƙananan yara, suna dawowa ne daga gonaki da bikin suna a lokacin da kwale-kwalen katako ya nutse.

Babban sakataren hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Adamawa, Dakta Mohammed Suleiman, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce lamarin ya faru ne da rana kuma ana ci gaba da aikin ceto.

Ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Fufore/Gurin a majalisar dokokin jihar Adamawa Hon. Barista Umar Bobbo Ismail, shi ma ya tabbatar da aukuwar lamarin.

KU KUMA KARANTA: Hatsarin kwale-kwale ya kashe mutane 12 a jihar Nassarawa

Wannan ci gaban ya zo ne sa’o’i 48 bayan da mutane takwas suka mutu a wani hatsarin jirgin ruwa a Rugange da ke ƙaramar hukumar Yola ta Kudu a Adamawa.

Mahmud, wani mai nutsewa a ruwa a yankin da ke cikin masu aikin ceto, ya ce za a iya hana aukuwar lamarin idan fasinjojin sun yi amfani da rigar ceto tare da aiwatar da wasu matakan kariya.

Ya kuma yi ƙira ga gwamnati da hukumomin da abin ya shafa da su tabbatar da kula da magudanan ruwa a kai a kai da kuma samar da na’urorin kariya irin su rigunan ceto domin hana aukuwar ɓarna a nan gaba.

Ɓarkewar hatsarin kwale-kwale ya haifar da damuwa game da tsaron lafiyar sufurin ruwa, musamman a lokacin damina.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...