No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar tsaro ta farin kaya, (DSS) ta kama tare da tsare mataimakiyar gwamnan babban bankin Najeriya mai kula da harkokin kuɗi, Aisha Ahmad, bisa zarge zargen damfarar hannun jari a bankin Polaris, Titan Bank da Union Bank.

Wata majiya a rundunar ‘yan sandan sirri ta shaida wa ‘News Point Nigeria’ cewa, a halin yanzu ana yi wa Mataimakiyar Gwamnan CBN tambayoyi kan yadda Bankin Titan Bank ya tara dala miliyan 300 don kammala sayan Bankin Union.

A cewar majiyar, sashen ya kuma ƙwace kayan lantarki na Ahmad tare da kwashe wasu takardu daga gidanta da ofishinta.

Har yanzu Ahmad tana nan a Sashen har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...