Guguwar Haikui ta mamaye yankin Taiwan, ta jiklata mutane da dama

Fiye da mutane 40 ne suka jikkata a Taiwan bayan da guguwar Haikui ta yi kaca-kaca a tsibirin, inda ta tumɓuke bishiyoyi tare da tilastawa dubban mutane barin wurin.

Guguwar wadda ta yi ƙasa a ranar Lahadi a gabar tekun gabas – ita ce ta farko da ta aukawa tsibirin kai tsaye cikin shekaru huɗu.

A cikin ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da iska mai ƙarfin gaske, mutane biyu a wani yanki mai tsaunuka sun ji rauni bayan wata bishiyar da ta faɗo ta aukawa wata mota.

Wasu da dama kuma sun jikkata, musamman ta hanyar faɗowar tarkace, in ji jami’ai.

A ranar Litinin, ma’aikatan tsaftace muhalli suna aiki don dawo da ayyuka bayan gidaje 160,000 sun rasa wuta ranar Lahadi. Sai dai kawo yanzu babu wani rahoto da ke nuna ɓarnar da aka yi a ginin.

KU KUMA KARANTA: Guguwa mai ƙarfi ta kashe mutane 11 a Pakistan

Ko da yake wannan lokacin guguwa ce a yammacin tekun Pasifik, wanda aka samu sau 11 ya zuwa yanzu, Haikui ita ce guguwar farko da ta taɓa kai wa Taiwan kai tsaye cikin shekaru huɗu.

Kasuwanci, makarantu da sauran wurare sun kasance a rufe a tsibirin, yayin da aka soke zirga-zirgar jiragen sama da na jirgin ruwa zuwa tsibiran da ke kewaye. Guguwar ta cika iskar da ta kai kilomita 200 (124 mph) amma babu wani ɓarna da aka samu ko kuma an samu asarar rayuka.

Yankunan kudanci da gabashin Taiwan sun fi fama da bala’in, yayin da babban birnin ƙasar Taipei dake arewacin tsibirin ya samu ruwan sama.

Gabanin faɗuwar guguwar, an kwashe sama da mutane 7,000 daga yankunan da hukumomi ke fargabar zaftarewar ƙasa da sauran rugujewar da guguwar ta haddasa.

A yanzu guguwar Haikui ta yi rauni zuwa mashigin zafi, ta kuma tashi zuwa mashigin Taiwan, inda ta nufi gaɓar tekun kudancin ƙasar Sin, inda za ta tashi a daren ranar Litinin da daddare.

Hakan na zuwa ne kwanaki biyu kacal bayan guguwar Saola, wacce ta zarce Taiwan amma ta haifar da hadari mafi girma a Hong Kong da kudancin China a tunkararta.

Guguwar ta isa a ranar Asabar, inda ta afkawa Hong Kong amma ɓarnar ba ta kai yadda ake zato ba.

Hukumomin ƙasar Sin a ranar Litinin ɗin nan sun tsawaita gargaɗi daga Saola zuwa Haikui yayin da sabuwar guguwar ta ke gabatowa, tare da yin ƙira ga jiragen ruwa da su shigo cikin teku da iska mai ƙarfi da kuma babban igiyar ruwa.


Comments

One response to “Guguwar Haikui ta mamaye yankin Taiwan, ta jiklata mutane da dama”

  1. […] KU KUMA KARANTA: Guguwar Haikui ta mamaye yankin Taiwan, ta jiklata mutane da dama […]

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *