No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnatin Zamfara ta sanar da rufe kasuwannin shanu guda takwas nan take a ƙananan hukumomi biyar na jihar.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai da al’adu Mannir Haidara ya fitar ranar Lahadi a Gusau.

Ya ce majalisar tsaron jihar ta amince da rufe kasuwannin shanu na wucin gadi yayin taron da ta gudanar a ranar Alhamis, 31 ga watan Agusta.

A cewarsa matakin na daga cikin matakan tunkarar sabbin hare-hare da satar shanu a sassan jihar.

“An ɗauki matakin ne biyo bayan sake ɓullar satar shanu da ake yi a yankunan da lamarin ya shafa.

“Kasuwannin shanun da abin ya shafa su ne: Danjibga da Kunchin-Kalgo a Tsafe; Kasuwan shanu na Bagega da Wuya a garin Anka. “Sauran su ne Dangulbi da Ɗansadau a Maru, Dauran a Zurmi da Nasarawar Burkullu a karamar hukumar Bukkuyim,” in ji Kwamishinan.

KU KUMA KARANTA: Likitoci a Zamfara sun dakatar da shiga yajin aiki

Haidara ya ce majalisar ta ɗorawa hukumomin tsaro da hukumar kula da lafiyar dabbobi da kiwo, da su tabbatar da bin doka da oda.

Ya jaddada ƙudurin gwamnatin Gwamna Dauda Lawal na maido da zaman lafiya a jihar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...