No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar sojin Gabon ta faɗa a ranar Asabar cewa za ta sake buɗe iyakokin ƙasar, waɗanda aka rufe sakamakon juyin mulkin da sojoji suka yi na hamɓarar da tsohon shugaban ƙasar Ali Bongo.

Mai magana da yawun sarakunan mulkin sojan Gabon ya faɗa a gidan talabijin na ƙasar cewa “sun yanke shawarar nan da nan don sake buɗe iyakokin ƙasa, ruwa da iska tun daga wannan Asabar”.

Wasu gungun sojojin ƙasar Gabon su 12 sun sanar a ranar Laraba cewa an rufe iyakokin ƙasar har zuwa wani lokaci, a wata sanarwa da aka watsa a tashar talabijin ta Gabon 24.

Janar Brice Oligui Nguema, shugaban jiga-jigan ‘yan jam’iyyar Republican Guard a ranar Laraba, ya jagoranci jami’ai a wani juyin mulki da aka yi wa shugaban ƙasar Ali Bongo Ondimba, ɗan gidan da ya shafe shekaru 55 yana mulki.

Korar tasa ta zo ne bayan da aka ayyana Bongo mai shekaru 64 a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasa a ƙarshen mako – sakamakon da ‘yan adawa suka yi wa laƙabi da maguɗi.

KU KUMA KARANTA: Sojoji sun sanar da Janar Nguema a matsayin shugaban ƙasar Gabon

Shugabannin juyin mulkin sun ce sun rusa hukumomin ƙasar tare da soke sakamakon zaɓen da kuma rufe kan iyakokin ƙasar. A ranar Litinin ne za a rantsar da Oligui a matsayin “shugaban riƙon ƙwarya”.

Wasu ƙasashe biyar a Afirka – Mali, Guinea, Sudan, Burkina Faso da Nijar – sun yi juyin mulki a cikin shekaru uku da suka gabata.

Sabbin sarakunan nasu sun ƙi amincewa da buƙatar da aka yi musu na ɗan gajeren lokaci na komawa bariki.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

3 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...