Connect with us

Labarai

NLC ta ayyana yajin aikin gargaɗi na kwana biyu kan cire tallafin mai

Published

on

Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC) ta fara shirin yajin aikin gargaɗi na kwanaki biyu daga ranar Talata 5 ga watan Satumba, domin nuna adawa da gwamnatin tarayya kan gazawarta na magance ƙalubalen da ke haifar da cire tallafin man fetur.

Shugaban ƙungiyar ta NLC, Joe Ajaero ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin da yake ganawa da manema labarai a gidan ma’aikata da ke Abuja, yayin da yake magana kan ƙudurin da kwamitin gudanarwa na NLC ya yi a ranar da ta gabata.

Ƙungiyar ƙwadagon dai na zargin gwamnatin tarayya da yin watsi da tattaunawar da kuma ka sa aiwatar da wasu ƙudurorin da suka cimma da gwamnatin a baya.

A ranar 2 ga watan Agusta, ƙungiyoyin ƙwadago sun nuna rashin amincewarsu da abin da suka bayyana a matsayin manufofin gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

KU KUMA KARANTA: Hukumar ‘yan Sanda sun gargaɗi NLC kan zanga-zangar da suka shirya yi

Ƙungiyoyin ƙwadagon Najeriya (NLC), Trade Union Congress (TUC) da ƙungiyoyinsu sun gudanar da zanga-zanga a babban birnin tarayya Abuja da jihohi da dama da suka haɗa da Legas, Abiya, Filato, Kaduna, Kano, Ribas, Zamfara, Katsina, Kuros Riba, Ebonyi, Inugu, Kwara, Ogun, Imo, Ondo, da Edo.

Zanga-zangar ta biyo bayan wa’adin kwanaki bakwai da aka bawa gwamnatin tarayya na neman “a gaggauta sauya duk wasu manufofin gwamnatin tarayya na yaƙi da talauci da suka haɗa da ƙarin farashin PMS (Premium Motor Spirit) da aka yi a baya-bayan nan, da ƙarin kuɗin makarantar gwamnati, da sakin watanni takwas da aka hana albashin malaman jami’a da ma’aikata”.

Ƙungiyar ta kuma buƙaci a sake duba mafi ƙarancin albashi daga N30,000 zuwa N200,000, tana mai cewa tun lokacin da Shugaban ƙasa ya yi jawabin rantsar da “Shugaban ƙasa” a ranar 29 ga Mayu, 2023, hankalin ‘yan Najeriya ya tashi.

Taro da dama da fadar shugaban ƙasa da ƙungiyoyin ƙwadago suka yi kan tallafin da ‘yan Najeriya ke fama da su sakamakon cire tallafin man fetur ya ci tura.

A watan da ya gabata, shugaban NLC, Joe Ajaero, ya bayar da hujjar cewa Naira biliyan 5 da aka amince wa kowace jiha da kuma babban birnin tarayya Abuja don rage tasirin cire tallafin man fetur bai isa ya yi tasiri ga jama’a ba.

Da yake bayyana a gidan talabijin na Channels Television’s Politics Today wanda ‘News Point Nigeria’ a ranar 18 ga watan Agusta ke sa ido a kai, Ajaero ya ce idan aka ƙididdige Naira biliyan 5 ba za ta kai Naira 1,500 ga kowane mutum ba.

A cewar sa, babu tabbas kan ko kuɗin rance ne ko kuma na jin daɗi ga jihohi ko kuma ga ‘yan Najeriya.

“Haɗin farko na farashin man fetur da kuma na ƙarshe ya motsa mutane da yawa daga kan iyaka zuwa matsanancin talauci,” in ji shi.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Likitoci a Zamfara sun dakatar da shiga yajin aiki | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Katsewar wutar lantarki sakamakon yajin aikin gargaɗin NLC – AEDC | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like