Connect with us

Labarai

Gwamnatin Yobe ta raba kayan abinci a Potiskum, don rage raɗaɗin rayuwa

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar (SEMA) a ranar Laraba ta raba kayan abinci ga marasa galihu a mutane 6,800 a ƙaramar hukumar Potiskum.

Dakta Mohammed Goje, Babban Sakataren Hukumar SEMA ya furta a wurin rabon kayayyakin cewa an yi hakan ne domin ƙara samar da abinci a tsakanin al’ummar jihar.
“Da zarar an samu yawo da abinci ko daga gwamnatin tarayya ko na jiha, ɗaiɗaikun mutane ko masana falsafa, za a rage wahalhalun da jama’a ke ciki.

“Yau a ƙaramar hukumar Potiskum domin rage raɗaɗin rayuwa ga masu ƙaramin ƙarfi tare da taimakon gaggawa, kamar yadda Gwamna Mai Mala Buni ya umarta.

“Muna yin niyya sama da masu cin gajiyar 6,800.
“Waɗanda suka amfana sun haɗa da mata, gidaje marasa galihu, masu fama da naƙasa, malaman firamare da sakandare.

KU KUMA KARANTA: Amfani da iskar gas na dafa abinci a janareta yana taimakawa masu ƙananan kanfanoni
“Ma’aikatan gwamnati, ɗalibai, dattijai, zawarawa, marayu da sauransu” in ji shi.

Goje ya lura cewa an fara rabon ne tun bayan da gwamnatin tarayya ta bayyana cire tallafin.
“Ayyukan ci gaba ne da gwamnati ke tafiyar da ita.

“Har yanzu za mu kai ga ƙarin al’ummomi har sai mun isa mutum na ƙarshe wanda ya kamata ya sami maganin,” in ji shi.
Ya kuma bayyana cewa an baiwa kowane magidanci kilogiram 20 na kwandon abinci. Ya shawarci waɗanda suka amfana da kada su sayar da kayan abinci ko raba kayan a wajen gidansu.
Hajiya Zainab Musa, ɗaya daga cikin waɗanda suka ci gajiyar tallafin ta miƙa godiyar ta ga gwamnatin Yobe, inda ta ce ɗaukar matakin ya zo a daidai lokacin da ya dace.

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like