Guguwar iska ta lalata gonakin kaji, ta kashe tsuntsaye dubu uku a Filato

0
177

Wata mummunar guguwa ta aukawa gidan kaji na Dauda Mafala da ke Rapomol a ƙaramar hukumar Barikin Ladi a jihar Filato a ranar Asabar ɗin da ta gabata, inda ta kashe tsuntsaye sama da 3,600.

Wakilin Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya, wanda ya ziyarci gonar a ranar Lahadi, ya gano cewa lamarin ya faru ne sakamakon mamakon ruwan sama da aka yi a yankin.

NAN ta ruwaito cewa guguwar ta lalata wasu gidajen kaji guda shida, wani ɓangare na katangar kaji da turakun wutar lantarki, da dai sauran gine-gine a gonar.

Manajan daraktan gonar, Keneth Mafala, ya shaida wa NAN cewa, gonar da aka kafa a shekarar 1976, tana da ƙarfin ɗaukar tsuntsaye 60,000.

Mista Mafala ya ce guguwar ta kuma lalata wani keji mai sarrafa kanta da ta kai dala 80,000.

“Da misalin ƙarfe 3:30 na rana a ranar Asabar, guguwar iska ta lalata gine-gine da dama a wannan gona.

KU KUMA KARANTA: Guguwa mai ƙarfi ta kashe mutane 11 a Pakistan

“Ya lalata wata gonar kaji da ke da tsuntsaye masu kwanciya 10,800. “Yayin da muke magana, mun yi asarar tsuntsaye 3,600, kuma kamar yadda kuke gani, muna ci gaba da kwashe su.

“Don haka, adadin na iya ƙaruwa da lokacin da muka gama. “Haka zalika gaba ɗaya ta lalata wani kejin kaji mai sarrafa kansa da ta kashe dala 80,000 da muka shigo da shi a shekarar 2013.

“Wannan injin yana da tsarin tattara ƙwai, tsarin ciyarwa da kuma tsarin dawo da taki,” in ji shi.

Mista Mafala ya kuma yi bayanin cewa baya ga kejin mai sarrafa kansa, jimillar ɓarnar da aka samu daga bala’in da ya kai sama da naira miliyan 250.

A martanin da mai magana da yawun ƙungiyar kiwon kaji ta Najeriya reshen Filato, Nanji Gambo ya mayar, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici.

Madam Gambo ta kuma ce babbar asara ce ga sana’ar kiwon kaji a jihar. Ta yi ƙira ga gwamnatin jihar da ta taimaka wa mai gonar.

Ta kuma bayyana buƙatar ganin gwamnati ta tallafa wa harkar kiwon kaji a jihar baki ɗaya.

A cewarta, sana’ar kiwon kaji na ɗaya daga cikin manyan masu ɗaukar ma’aikata a ƙasar.

“Tuni sana’ar kiwon kaji na fuskantar ƙalubale iri-iri saboda taɓarɓarewar tattalin arziƙin da ƙasar nan ke fuskanta. “Haƙiƙa cire tallafin yana magana kan manoman kaji.

“Akwai tsadar kayan abinci, rashin kasuwan ƙwai da sauran kayan kiwon kaji da sauran ƙalubale.

“A shekarar da ta gabata, alal misali, da yawa daga cikin manoman mu sun fuskanci ambaliyar ruwa da ta addabi wasu al’umma a jihar kuma babu wani tallafi da ya zo musu.

“Don haka muna ƙira ga gwamnati da ta tallafa wa wannan manomi da sauran manoman da irin wannan yanayi ya shafa domin farfaɗo da sana’o’insu.

“Ta haka ne za su koma kasuwanci tare da ba da gudummawa ga ci gaban tattalin arziƙin jihar,” in ji Misis Gambo.

Ta kuma yi ƙira ga Gwamnatin Filato da ta yi amfani da wani ɓangare na tallafin naira biliyan biyar da Gwamnatin Tarayya ta ware domin farfaɗo da sana’ar kiwon kaji da ta addabi jihar.

Leave a Reply