No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

A jihar Kano an gabatar da Salloli tare da ruwan addu’o’i, kan halin matsin rayuwa da al’umma suke ciki a Najeriya. A yau Lahadi da safe ne, al-ummar ƙaramar hukumar Ungogo da ke jihar Kano, suka sake fita masallacin idi suka gabatar da Salloli tare da yin ruwan addu’o’i, domin Allah ya kawo mana ƙarshen musifa ta tsadar rayuwa, tsadar kayan masarufin da ake ciki wanda ba a taɓa yin irin sa ba a Najeriya.

Limamin da ya jagoranci addu’ar, ya yiwa Mutane nasihohi masu ratsa zuciya kan mutane su koma ga Allah, a daina saɓo, a taimaki mutanen da suke cikin mayuwancin hali. Limamin yace, yauce rana ta biyu gobe Litinin ma za su sake fita su ci gaba da gabatar da addu’o’in.

Mu ma muna Addu’ar Allah ya amsa addu’o’in da suka gabatar. Ya kamata sauran gagaruwa ma, su fara gabatar da irin waɗannan addu’o’in, domin wahalar da ake sha ya wuce duk yadda ake tunani.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...