Connect with us

Labarai

Ba mu amince Sojojin Najeriya su yaƙi Nijar ba – Majalisar Dattawa

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Majalisar dattawa ta yi fatali da yunƙurin ɗaukar matakin amfani da ƙarfin soji a kan Jamhuriyar Nijar.

Majalisar ta yi ƙira ga membobin ECOWAS da sauran shugabanni da su yi tir da juyin mulki a ƙasar tare da tashi tsaye wajen daidaita lamura ta sigar da ya dace.

A cewar majalisar akwai buƙatar ɗaukar matakan laluma da zurfin tunani wajen shawo kan rigimar shugabanci da ke faruwa a Nijar.

A ranar Juma’a ne shugaba Tinubu ya rubuta wasiƙa ga majalisar yana neman amincewarta kan aiwatar da matsayar da shugabannin ECOWAS suka cimma a kan halin da ƙasar Nijar ke ciki.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Najeriya har yanzu ba su samu umarnin shiga tsakani a Nijar ba – DHQ

A jawabin ECOWAS da shugabanta, Bola Ahmed Tinubu ya fitar, ya ce ɗaukar matakin ƙarfin soji ne kawai zai kawo ƙarshen juyin mulkin da sojoji suka yi a Nijar.

A yayin zaman majalisar a ranar Asabar, Sanata Bamidele Opeyemi, ya bijiro da batun tare da nuna adawa da matakin ƙarfin Soja, inda majalisar ta cimma matsayar ƙin amincewa da matakin tare da neman shugaban Nijeriya da ya ƙara azama wajen ganin an shawo kan rikicin ta hanyar tattaunawa.

Da yake magana bayan zaman da majalisar ta yi a sirrance na tsawon awa biyu, shugaban majalisar, Godswill Akpabio, ya ce ba su amince a ɗauki matakin Soja kan Nijar ba ne saboda kyakkyawar alaƙa da ta jima a tsakanin Nijar da Nijeriya.

“Zaman namu, majalisa ta yi tir da juyin mulkin da ya wakana a jamhuriyyar Nijar.

“Majalisa ta jinjina wa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da sauran shugabanni ECOWAS bisa ɗaukan matakin gaggawa kan lamarin.”

Ya ce, amma Tinubu ya bi matakin tambayar majalisar domin zuwa ga fagen yaƙi domin aiwatar da matsayar da ECOWAS ta cimma, “Jagorancin majalisa za ta samu shugaban ƙasan domin faɗa masa matakin da ya dace a ɗauka domin shawo kan wannan lamarin domin tabbatar ba a lalata alaƙar da ke tsakanin Nijar da Nijariya ba,” Akpabio ya shaida.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like