No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ce jami’anta sun fatattaki ‘yan bindiga da suka kai hari ofishin ‘yan sanda na yankin ƙaramar hukumar Zurmi a jihar.

Rundunar ta ce ta kuma kama wata mata mai shekaru 35 da ake zargi da bayar da bayanai.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan, ASP Yazid Abubakar ya bayyana hakan a ranar Juma’a a wani taron manema labarai a Gusau.

Mista Abubakar ya ce jami’an ‘yan sandan da ke aiki a ofishin ‘yan sandan sun yi aiki ne bisa sahihin bayanan sirri na cewa wasu gungun ‘yan bindiga na shirin kai harin.

“Jami’an ‘yan sanda sun haɗa kai, suka tunkari ‘yan bindigar tare da yin artabu da su da bindiga wanda ya ɗauki tsawon sa’o’i ana gwabzawa.

KU KUMA KARANTA: Sojojin Najeriya suna da karfin daƙile tayar da ƙayar baya – COAS

“Sakamakon haka, an kashe ɗaya daga cikin ‘yan bindigar yayin da sauran suka tsere zuwa cikin daji suna zubar da jini a kan hanyarsu saboda raunukan da suka samu.

“Binciken da ‘yan sanda suka yi bayan faruwar lamarin, sun kama wata mata ‘yar shekara 35 da ake zargin mai ba da labari ce daga ƙauyen Rukudawa.

“Waɗanda ake zargin ta amsa cewa tana aiki da ɗan bindiga Ɗankarami Gwaska a matsayin mai ba shi labarin kuma ta ba ta aikin sa ido a ofisoshin ‘yan sanda.

“An ƙwato wayar hannu guda biyu ɗauke da lambobin wayar ‘yan fashi a hannunta,” in ji Mista Abubakar.

“A ranar 28 ga watan Yuli ne ‘yan sanda da ke aiki tare da 34 PMF, waɗanda aka tura yankin Magarya da ke ƙaramar hukumar Zurmi, sun yi aiki da rahoton leƙen asirin cewa wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne na kan hanyarsu ta kai wa Musulmai hari a lokacin Sallar Juma’a a ƙauyen Kwata da ke gundumar Magarya.

“Jami’an ‘yan sanda sun tunkare su inda suka yi nasarar daƙile harin, ‘yan bindigar sun tsere zuwa cikin daji.

“Bindigu AK47 guda biyu, alburusai 7.62 harsashi huɗu da kuma babur Bajaj a wurin da lamarin ya faru, yayin da rundunar ta ci gaba da bin sawun waɗanda ake zargin da zummar kama su tare da gurfanar da su gaban ƙuliya.

“A ranar 27 ga watan Yuli da misalin ƙarfe 13:30 na safe, rundunar ‘yan sandan da ke yankin Gusau ta gudanar da bincike kan bayanan sirri da suka kai ga kama wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne da masu garkuwa da mutane da suka addabi yankin Saminaka da ke cikin garin Gusau,” in ji kakakin rundunar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...