No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hedikwatar tsaro ta ce har yanzu rundunar sojin Najeriya ba ta samu umarni na tsoma bakin soja a jamhuriyar Nijar bayan juyin mulkin da ya kai ga hamɓarar da mulkin dimokraɗiyya a ƙasar.

Daraktan yaɗa labarai na tsaro, Birgediya janar Tukur Gusau, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, ya yi watsi da rahoton da aka buga ta yanar gizo cewa sojojin Najeriya na haɗa dakarunsu domin ɗaukar matakin soji a Jamhuriyar Nijar.

A cewarsa, har yanzu ƙungiyar ta AFN ba ta samu wani umarni daga hukumar da ta dace ba na fara ɗaukar matakin soji kan gwamnatin mulkin soja a Nijar.

KU KUMA KARANTA: Nijar ta shiga matsalar lantarki bayan katsewa daga Najeriya

“Ba labari ne cewa wasu daga cikin sojojin Jamhuriyar Nijar sun ƙwace mulki daga hannun zaɓaɓɓiyar gwamnati ta hanyar da ta saɓawa tsarin mulkin ƙasar.

“A game da wannan karyewar gwamnati ba bisa ƙa’ida ba, shugabannin ECOWAS sun gana, kuma an cimma wasu zaɓuka kan yadda za a shiga cikin rikicin.

“Zaɓin soji shi ne zaɓi na ƙarshe da za a ɗauka idan duk wani zaɓin ya gaza, a sauya yanayin da kuma mayar da gwamnatin Jamhuriyar Nijar kan tsarin mulki.

“A halin yanzu, kwamitin hafsan hafsoshin tsaro na ƙungiyar ECOWAS na gudanar da wani taro na musamman a Abuja domin tattaunawa kan al’amuran siyasa a jamhuriyar Nijar tare da miƙa shirinsu ga kwamitin shugabannin ƙasashen ƙungiyar ECOWAS domin tantancewa.

“A ƙarshe, Rundunar Sojin Nijeriya ba za ta iya ci gaba da gudanar da duk wani aiki a kowace ƙasa ta ECOWAS ba tare da izini daga Hukumomin Shugabannin Ƙasa da na Gwamnati ba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

3 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...