Connect with us

Labarai

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da fasinjoji tara, sun kashe biyu a Inugu

Published

on

Wasu ‘yan bindiga da ke aiki a layin Imo na babbar titin Inugu zuwa Fatakwal, sun yi garkuwa da wasu fasinjoji 9 da ke kan hanyar zuwa Enugu, inda suka kashe biyu tare da yi wa wasu fashi.

Waɗanda aka kashen ‘yan asalin garin Amangwo Olokoro ne a Umuahia, an ce sun tafi Enugu ne ranar Asabar don yi musu jana’iza, lokacin da wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka kai musu hari.

Da yake bayyana halin da suke ciki ga Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya a Umuahia a ranar Lahadi, ɗaya daga cikinsu wanda ya bayyana sunansa da Francis, ya ce an harba motar su ƙirar Sienna da bindiga a kusa da mahaɗar Arondizuogu da ke kan babbar hanyar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kashe masu haƙa ma’adinai a jihar Filato

Francis (ba sunansa na gaskiya ba) ya ce daga baya aka karkatar da motar daga kan titin Arondizuogu da ke Imo, inda aka kai su wata katafariyar daji mai nisa.

Ya ce: “Ban taɓa samun irin wannan yanayin a rayuwata ba. “Muna tafiya Enugu ne don yin jana’iza, lokacin da muka isa kusa da Junction Arondizuogu, sai muka ga wasu gungun ‘yan bindiga ɗauke da muggan makamai, suka ce mu yi mu tsaya da motocinmu.

“Ɗaya daga cikinmu da ke cikin motar ya tambaye su ‘Me ya sa kuke neman mu yi parking kuna nuna mana bindigogi, kun san ko ni wane ne?’.

“Sai wani daga cikin ‘yan iskan ya ce, ‘yanzu oga za ka tabbatar mana da wane ne kai.

“Sun umarce mu da fitowa daga cikin motar kuma suka ce mu zauna a ƙasa mu cire rigarmu da suka rufe mana idanu da su.

“Daga nan ne suka fara dukan mutumin da ya yi wannan tsokaci da adduna,” in ji Mista Francis.

Ya ce lokacin da suka shiga unguwar, mazauna garin “suna kallon mu kamar suna kallon bidiyo.

“Lokacin da muka sauƙo daga motar, shugabansu ya tambaye shi game da mutumin da ya yi tsokaci, suka nuna masa.

“Sun fito da shi, kuma da ƙyar taku uku daga gare mu, sai suka harbe shi ya mutu har lahira.

“Wani mutum da ke tare da mu, wanda ya ga abin da ya faru kuma ya yi yunƙurin tserewa an garzaya da shi, aka kuma harbe shi,” in ji Francis.

A cewarsa, sun kama gawarwakin biyu. Ya ce maharan ba su gaza 50 a maɓoyar su ba, kuma 20 daga cikinsu ɗauke da manyan makamai.

“Kuma abin da ya fi ban dariya shi ne cewa waɗannan mutane suna magana da yarenmu.

“Sun gaya mana cewa mutanen Umuahia ‘sabo ne a gare su’, sun ce ka da mu kaɗa ƙuri’a a zaɓen da ya gabata kuma mun fito zaɓe.

“Cewa sun ayyana ranar Litinin a zauna a gida kuma ba ma yi musu biyayya. “Duk mutumin Umuahia da suka samu a nan zai yi zafi.

“Sai suka nemi mu yi addu’o’inmu na ƙarshe,” in ji Francis.

Ya ce suna cikin addu’o’in ne aka shigar da su ɗaya daga cikin sabbin motocin ƙirar ‘Hummer’ guda uku da ke cikin maɓoyar sannan aka kai su inda a ƙarshe suka loda su a cikin motar su ta Sienna suka kai su hanyar da ta kwalta.

“A nan ne suka tambaye mu ko za mu iya nemo hanyarmu, muka ce a’a, sai suka ce wa direban ya miƙe.

“Sun ce mu je mu gaya wa mutanen Umuahia abin da muka gani. “Hakan ne muka samu kanmu zuwa Umuahia,” in ji shi.

Mista Francis ya ce kayayyakin da aka karɓa daga wajensu, sun haɗa da kudi da wayoyin hannu.

A halin da ake ciki dai, waɗanda suka mutun an bayyana sunayensu da Fasto Chukwuemeka Nwachukwu, wanda ya yi tsokaci bayan an ba su tuta, da kuma shugaban matasan ƙauyen, Ifeanyi Onwunkwe, wanda ya yi yunƙurin tserewa.

Wani ɗan jarida daga yankin ya ce bisa sharaɗin ɓoye sunansa cewa “al’amarin baƙin ciki ya jefa yankin cikin makoki”.

Ƙoƙarin samun tabbacin harin daga jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan Imo, ASP Henry Okoye, ya ci tura, saboda ƙiran wayar da aka yi masa ya gagara gamuwa da shi.

Sai dai wani babban jami’in ‘yan sanda a hukumar ‘yan sandan jihar Abia ya yi iƙirarin cewa yana sane da faruwar lamarin amma ya ce har yanzu ba a kai ga shiga ba.

“Ina sane da harin na ranar Asabar amma kun san lamarin ya faru ne a Imo.

“Don haka, yayin da muke magana, babu wanda ya shiga nan a hukumance,” in ji majiyar.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Masu garkuwa da mutane sun kashe mata mai shekaru 60 bayan sun karɓi kuɗin fansa miliyan ɗaya | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Published

on

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Shugabannin soja na yankin Sahel suna gudanar da taro a Nijer, yayin da ECOWAS ke taro a Najeriya

Afirka ta Yamma mai rarrabuwan kai ta gudanar da tarukan ƙolin shugabannin ƙasa guda biyu a ƙasashe daban-daban biyu a ƙarshen makon, inda aka gudanar da taro farko ranar Asabar a Nijar tsakanin shugabannin mulkin soja na yankin Sahel.
A gefe guda kuma za a gudanar da wani taron ƙoli ranar Lahadi a Najeriya inda shugabannin sauran ƙasashe mambobin ƙungiyar tattalin arziƙin yankin ta ECOWAS za su hallara.

Taron ƙolin da ake yi yau Asabar a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar, zai kasance karo na farko tsakanin shugabannin sojojin sabuwar ƙungiyar haɗin kan yankin Sahel wato Alliance of Sahel States ko kuma AES.

Mali, Burkina Faso da Nijar su ne suka kafa yarjejeniyar kare juna a watan Satumba, waɗanda suka bar babbar ƙungiyar ECOWAS a cikin watan Janairu.

Ficewar su daga ECOWAS, wani ɓangaren ya samo asali ne daga zargin da suke yi cewa Paris tana yiwa ƙungiyar katsalandan kana ba ta ba da taimakon da ya kamata a yaƙi da masu iƙirarin yaƙin jihadi.

Ficewar ta sa ƙasashen uku sun janye kansu daga Faransa da ta yi musu mulkin mallaka, suka kori sojojin Faransa masu yaƙi da masu iƙirarin jihadin kana suka juya zuwa ga ƙasashen da suke ƙira da aminan gaskiya, da suka haɗa da Rasha da Turkiya da kuma Iran.

KU KUMA KARANTA:Shugabannin Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa ƙungiyar haɗaka

Idan aka yi la’akari da munanan tashe-tashen hankula na ‘yan jihadi da ƙasashen uku ke fuskanta, “yaƙin da ta’addanci” da “ƙarfafa haɗin gwiwa” za su kasance kan ajandar taron ƙolin na yau Asabar, a cewar fadar shugaban ƙasar Burkina Faso.

Taron ƙolin da za a gudanar ranar Lahadi a Abuja zai ba shugabanni a ƙasashen ECOWAS damar tattaunawa a kan irin alaƙa da za su ƙulla da ƙungiyar ta AES.

Bayan wasu tarurrukan da suke yi tsakanin ƙasashe biyu, shugabannin uku na yankin Sahel sun yi taro a karon farko tun bayan da suka hau karagar mulki ta hanyar juyin mulki tsakanin shekarar 2020 zuwa 2023.

Continue Reading

Labarai

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Published

on

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

 

Nan da 2030 za a fuskanci matsananciyar yunwa a Nijeriya — Majilisar Ɗinkin Duniya

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi gargaɗin cewar ‘yan Najeriya miliyan 82, kimanin kashi 64 na ‘yan ƙasar ka iya fuskantar matsalar yunwa nan da shekarar 2030.

Haka kuma MƊD ta yi ƙira da gwamnatin ƙasar ta magance matsalar sauyin yanayi da matsalar ƙwari da sauran abubuwan da yi wa harkar noma barazana.

Jaridun Najeriya sun ambato jami’in Majalisar Ɗinkin Duniyar, Taofiq Braimoh – wanda ya wakilci kodinetan ayyukan jin ƙai na hukumar abinci da ayyukan noma na majalisar na bayyana haka lokacin da yake jawabi kan matsalolin ƙarancin abinci a taron ƙaddamar da shirin bunƙasa ayyukan noma na ‘CropWatch’ a birnin Abuja.

KU KUMA KARANTA:Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi maraba da sakin yara 21 da aka yi garkuwa da su

Mista Braimoh ya ce akwai buƙatar gwamnatin Najeriya ta ɗauki matakan da suka dace cikin gaggawa don magance matsalar.

“Gwamnatin Najeriya tare da haɗin gwiwa masu ruwa da tsaki, sun gudanar da bincike na shekara-shekara da suka saba gudanarwa kan abinci. Sakamakon binciken ya tayar da hankali, kimanin mutum miliyan 82 ne za su fuskanci yunwa nan da 2030,” kamar yadda Jaridun ƙasar suka ambato Braimoh na bayyanawa.

Ya ci gaba da cewa matsalar rashin abinci da ƙasar ke fama da shi, baya rasa nasaba da matsalar sauyin yanayi da duniya ke fama da ita, da matsalar ƙwari da wasu abubuwa da ke yi wa harkar noma barazana a ƙasar.

Hasashen na Majalisar Ɗinkin Duniyar na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsadar abinci, lamarin da ya tilasta wa gidaje da dama haƙura da sayen abincin da suka saba ci.

A cikin rahotonta baya-bayan nan, hukumar ƙididdigar ƙasar ta ce farashin abinci a ƙasar ya ƙaru zuwa kashi 40.66 a watan Mayu, matakin da aka jima ba a ga irinsa ba.

Continue Reading

Labarai

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Published

on

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta maka jaridar Daily Trust a kotu, tare da shigar da ƙorafi game da ita, a gaban ƙungiyar masu gidajen jarida ta Najeriya saboda abin da ta ƙira ”yaɗa kalaman neman tayar da rikici da karya aikin jarida”

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tana sane da yadda a cikin ‘yan watannin baya, jaridar Daily Trust ke yaɗa labaran da ke neman gogawa gwamnatin kashin kaji.

Da ya ke magana a wajen wani taron manema labarai a ranar Asabar, ministan yaɗa labaran ya kafa hujja da labaran da jaridar Daily Trust ta wallafa a game juyin mulkin Nijar, da wanda ya ce jaridar ta rubuta a kan shirin sauya sunan titin Murtala Muhammad da ke Abuja zuwa Wole Soyinka da kuma na baya bayan nan a game da sanya hannu a kan yarjejeniyar da ta shafi amincewa da auren jinsi.

KU KUMA KARANTA: Alaƙar soyayya tsakanin jinsi ɗaya ta haramta a Iraƙi

Ya yi bayanin cewa a dukkan labaran, gwamnatin ta gano yadda jaridar ta bayar da rahoto ba tare da gabatar da hujja ko shaidun zargin da ta yi ba, lamarin da kuma gwamnatin ke kallo a matsayin wani yunƙuri na wallafa ƙarya domin tunzura jama’a.

Ya ce: ‘’Ba mu taɓa tunanin Daily Trust da mutanen da ke da ita za su kai wannan mataki ba wajen neman tayar da rikici a ƙasar nan, ta hanyar zargin cewa gwamnati ta sanya hannu a kan yarjejeniyar tallata auren jinsi. Wannan tsabar zalunci ne saboda babu wannan tanadi a cikin yarjejeniyar.’’

Ministan ya koka da yadda wannan labarin ya janyo huɗuba mai zafi daga wasu malaman addini da kuma jefa jama’a cikin halin ɗarɗar, wanda kuma ya ce jaridar ce ta janyo.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

Saboda haka, ministan ya ce ‘’Gwamnatin tarayya za ta bi duk hanyoyin da doka ta amince da su, domin neman haƙƙi a kotu.’’

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like