No menu items!

Sample Page Title

Date:

An yi fargabar mutuwar mutane biyar a ranar asabar bayan da wani jirgin ruwa mai sauri ya kife a mashigin ruwan Kalaba.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya bayar da rahoton cewa, jirgin ya kife ne a hanyarsa ta zuwa Oron a Akwa Ibom.

Wani babban jami’in sojan ruwa da ke aiki da rundunar sojojin ruwa ta Gabashin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kuma ce rundunar ta taka rawar gani wajen ceto wasu daga cikin waɗanda harin ya rutsa da su.

“Rundunar sojin ruwa sun shiga aikin ceto; a ƙalla mun ceto 14 daga cikinsu.

KU KUMA KARANTA: Mutane huɗu sun mutu, da dama sun jikkata a hatsarin mota a hanyar Ibadan

“Ba zan iya ba ku ainihin matsayin jirgin ba saboda kawai mun garzaya ne don aikin ceto, amma na tabbata nan ba da jimawa ba rundunar za ta fitar da wata sanarwa kan hakan,” in ji shi.

NAN ta tattaro cewa mutane 20 ne suka shiga jirgin a Marina a Kalaba.

Duk da haka, ya kife da mintuna bayan ya tashi daga filin jirgin ruwa na Kalaba Marina.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...