No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya kammala ziyarar aiki da ya kai birnin Paris na Faransa, inda kuma zai wuce birnin Landan a yau Asabar, kamar yadda fadar shugaban ƙasar ta bayyana.

Tun farko an tsara Tinubu zai koma gida Abuja ne bayan kammala taron, wanda shugabannin Afirka suka tattauna harkokin kasuwanci da zuba jari a nahiyar.

“Sai dai yanzu zai wuce birnin Landan na Birtaniya don yin wata ziyara ta ƙashin-kansa,” a cewar sanarwar.

Ta ƙara da cewa shugaban zai koma gida kafin bikin Idin Babbar Sallah, wanda za a fara ranar Laraba.

A ranar Talata Tinubu ya tafi Paris bisa rakiyar wasu daga cikin masu ba shi shawara.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...