Connect with us

Labarai

Wasu ‘yan bindiga sun kashe ma’aikacin INEC, sun sace matarsa a Ebonyi

Published

on

Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton masu garkuwa da mutane ne sun kashe ma’aikacin hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) a jihar Ebonyi.

Wanda aka kashe, Emnanuel Igwe, mataimakin jami’in zaɓe, AEO, an kashe shi ne a hanyar Ishiagu na hanyar Ishiagu zuwa Mpu a yammacin Lahadin da ta gabata yayin da yake dawowa daga jihar Anambra.

An kuma bayyana cewa ‘yan bindigar sun sace matar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kashe basaraken gargajiya da ‘ya’yansa huɗu, sun sace shanu 100 a Kaduna

Jami’in hulɗa da jama’a na ‘yan sandan, SP Onome Onovwakpoyeya, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Litinin a Abakaliki, ya ce an aike da tawagar ƙwararrun ‘yan sanda domin farauto masu laifin.

Ta ce: “Eh, an kai harin inda aka harbe mutum ɗaya a ka ta fuskar gilashin, kuma ba a ɗauke komai daga cikin motar, kuma ɗayan da aka kashen wani manomi ne da ke aiki a gonarsa wanda suka yanke maƙogwaro.

Wasu ’yan asalin yankin Ishiagu da ke ƙaramar hukumar Ivo ta Jihar Ebonyi a Abakaliki, waɗanda suka mayar da martani kan lamarin a hirarsu da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, sun yi ƙira ga ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro da su daƙile matsalar tsaro da ke kunno kai a kan hanyar Ishiagu zuwa Mpu.

Shugaban matasan Ohanaeze Ndigbo, Cif Damian Okoafor, wanda ya tabbatar da kisan mahaifinsa ga manema labarai a Abakaliki a ranar Litinin, ya ce wasu da ake zargin makiyaya ne suka mamaye al’umma a ranar lahadin da ta gabata kuma suka aikata wannan mummunan aiki.

“Waɗanda ake zargin makiyaya ne suka sake kai hari a unguwar Ishiagu, suka kashe mahaifina, wani mutum ɗaya sannan suka sace daya,” inji shi.

Nicholas Onu, ma’aikacin hukumar zaɓe ta INEC a hedikwatar Abakaliki, ya bayyana cewa wanda aka kashe abokin aikinsu ne, yana mai cewa hasarar ta yi yawa.

Ya yi ƙira da a gaggauta tura tawagar jami’an tsaro na haɗin gwiwa na ‘yan sanda da sojoji domin daƙile sace-sacen mutane da fashi da makami da sauran miyagun laifuka a kan hanyar.

“Masu garkuwa da mutane da ake zargin makiyaya ne sun harbe Mista Emmanuel Igwe har lahira a lokacin da suka yi awon gaba da matarsa.

“Bayanin bayanan da ‘yan uwa suka samu sun nuna cewa an kwashe gawar an ajiye ta a ɗakin ajiye gawa da ke Abakaliki yayin da waɗanda ake zargin ke neman kuɗin fansa naira miliyan 10,” in ji Mista Onu.

Dokta Innocent Mbazu, malami a Kwalejin Ilimi ta Jihar Ebonyi, Ikwo, wanda ke zaune a Abakaliki, ya buƙaci ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro su shiga tsakani cikin gaggawa, yana mai bayyana lamarin a matsayin ‘abin takaici.

“An yi garkuwa da wani direban mota tare da kashe wani ɗan uwanmu a gonarsa a ranar Lahadi a kan titin Ishiagu na hanyar Ishiagu zuwa Mpu.

“Duk wanda ke da niyyar amfani da hanyar ya kamata ya yi kasuwanci da hankali ko kuma ya guje wa hanyar a yanzu idan zai yiwu.

Da alama masu garkuwa da mutane da ke aiki a kan babbar hanyar Amaeze-Awgu sun koma ta Mpu.

“An ce mutanen Ngwogwo a Ishiagu suna zanga-zanga a halin yanzu. Allah ya taimake mu!!,” Mbazu ya koka.

3 Comments

3 Comments

  1. Pingback: Su waye suka sace fitilun titin tashan jirgin sama na Legas? | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Su waye suka sace fitilun titin tashan jirgin sama na Legas? - LEGEND FM DAURA

  3. Pingback: ‘Yan sanda sun tabbatar da sakin Rabaran Father da aka sace a Ebonyi | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like