Connect with us

Labarai

Gwamnatin jihar Kano za ta biya wa ɗalibai 55,000 kuɗin rubuta jarabawar NECO

Published

on

Ɗaya daga cikin manufofin gwamnatin jihar Kano na mayar da ɓangaren ilimi matsayi da kuma ba shi kulawar da ake buƙata, gwamnan jihar Injiniya Abba Kabir Yusuf ya amince da biyan kuɗin NECO ga ɗaliban makarantun gwamnati su dubu hamsin da biyar (55,000) nan take domin samun damar rubuta jarabawar SSCE (NECO) a shekarar 2023.

A wata sanarwa da babban sakataren yaɗa labaran gwamnan jihar Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar lahadi, ya ce gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai wasu nasarorin da gwamnatinsa ta samu a cikin kwanaki ashirin da suka gabata a gidan gwamnati.

Injiniya Abba Kabir Yusuf ya buƙaci ɗaliban da suka amfana da su yi aiki tuƙuru don ganin an samu sakamako mai kyau sannan kuma su mayar da hankali wajen ganin sun tabbatar da ɗimbin jarin da gwamnatin jihar ta yi don gudun ka da su daina neman ilimi.

KU KUMA KARANTA: JAMB ta biya biliyan 1.5 ga cibiyoyin shirya jarabawa ta CBT

A cewar Gwamnan, “A matsayina na gwamnatin da abin ya shafa, mu tabbatar da cewa ba a daina ci gaban karatun ku na neman ilimi ba, kuma nan take na amince da biyan kuɗin jarabawar ga ɗalibai dubu 55,000 a faɗin jihar nan.

Ya kamata ku yi iya ƙoƙarinku kuma ku jajirce domin ku fito da kyakkyawan sakamakon jarrabawar da za ku iya farantawa jihar da iyalanku da kuma alfahari da ku” Gwamnan ya yi gargaɗi.

Ya kuma tabbatar wa al’ummar Kano cewa gwamnatinsa na fito da manufofi da tsare-tsare na inganta harkar ilimi, domin ilimi shi ne ginshiƙin ci gaban kowace al’umma.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Sanata Yari ya raba raguna 500 ga maƙwabta | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like