Connect with us

Labarai

‘Yan sanda a Zamfara sun bi umarnin kotu, sun mayar wa da tsohon gwamna motocin sa

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara a ranar Asabar ɗin da ta gabata ta ce ta mayar da dukkan motocin da ta kama daga hannun tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, ASP Yazid Abubakar, ya tabbatar wa Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya faruwar lamarin a ranar Asabar ta hanyar tattaunawa ta wayar tarho.

Abubakar ya ce an mayar da motocin ne bisa bin umarnin babbar kotun tarayya da ke Gusau.

Kotun ƙarƙashin jagorancin Mai shari’a Aminu Bappah-Aliyu, ta bayar da umarnin a ranar 15 ga watan Yuni, ta umurci dukkanin hukumomin tsaron da suka kwashe motocin da ke gidajen Matawalle da ke Gusau da Maradun, da su mayar da su cikin sa’o’i 48.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin Zamfara ta bai wa Matawalle wa’adin mayar da motocin alfarma na biliyoyin nairori

NAN ta ruwaito cewa jami’an tsaro sun kwashe motocin daga gidajen biyu bisa umarnin gwamnatin jihar. Kotun ta bai wa duk wanda ke da hannu a harin da aka kai wa gidajen tsohon gwamnan wa’adin sa’o’i 48 domin su bi wannan umarni.

“Eh, rundunar ‘yan sanda ta bi umarnin kotu dangane da mayar da dukkan motocin tsohon gwamna Bello Matawalle.

“Mun mayar da dukkan motocin zuwa harabar babbar kotun tarayya da ke Gusau, kamar yadda nake magana da ku a yanzu, babu wata mota guda da ke hannun ‘yan sanda,” in ji Abubakar.

Kotun ta kuma bayar da umarnin dakatar da waɗanda ake ƙara a ƙarar da Matawalle ya shigar a gaban kotu daga ɗaukar wani mataki na gaba dangane da lamarin.

Waɗanda suka amsa sun haɗa da Sufeto-Janar na ‘yan sandan Najeriya da kuma kwamishinan ‘yan sandan jihar Zamfara.

Sauran sun haɗa da hukumar tsaro ta farin kaya, (SSS), da kuma jami’an tsaron farin kaya na Najeriya, (NSCDC). Kotun ta kuma umarci jami’an tsaro da su nesanta kansu daga duk wani mataki da za a ɗauka, har zuwa lokacin da za a saurari ƙarar da kuma yanke hukunci a gabanta.

Suleiman Idris, mai magana da yawun Gwamna Dauda Lawal na Zamfara, ya ce an ƙwato fiye da motoci 40 a gidajen tsohon gwamnan guda biyu.

Ya kuma tabbatar da cewa hukumomin tsaro sun ɗauki matakin ne bisa umarnin gwamnatin jihar.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Hukumar DSS ta saki tsohon Gwamnan Zamfara, Yari | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like