No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sanda a jihar Ondo ta tabbatar da yin garkuwa da Ibrahim Bodunde-Oyinlade, babban limamin ƙungiyar USO a ƙaramar hukumar Owo ta jihar.

An yi garkuwa da babban Imam mai shekaru 67 a gonarsa da ke ‘Asolo Farm Camp’ da yammacin ranar Asabar.

Wani ɗan uwa ya ce sun kai rahoto ga ‘yan sanda lokacin da Bodunde-Oyinlade bai dawo gida ba da ƙarfe biyu na rana kuma ba a amsa ƙiran wayarsa.

“Masu garkuwa da mutanen sun tuntuɓi dangin amma har yanzu ba su nemi a biya su kuɗin fansa ba,” in ji shi da sharaɗin a sakaya sunansa.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun kama mai bawa masu garkuwa da mutane labari a Abuja

Sai dai kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Olufunmilayo Odunlami-Omisanya, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce ’yan sanda da ’yan banga suna tseguntawa dajin suna neman babban Limamin.

Mista Odunlami-Omisanya ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya cewa an gano motar mamacin da wayar salula a gonar.

“Da misalin ƙarfe 6 na yamma ne ‘yan uwa suka zo ofishin ‘yan sanda da ke unguwar USO.

Ya ƙara da cewa “DPO, ‘yan sanda da ƴan banga suna bincike a yankin domin samun ceto.”

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...