No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Filato ta ceto ɗalibai shida daga cikin bakwai na jami’ar Jos da wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su ranar Litinin.

DSP Alfred Alabo, kakakin rundunar ‘yan sandan ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a a Jos.

A cewar Mista Alabo, an ƙubutar da biyar daga cikin ɗaliban, yayin da ɗaya ya tsere daga hannun masu garkuwa da mutanen.

“Rundunar ‘yan sanda na farin cikin sanar da jama’a cewa shida daga cikin bakwai da aka yi garkuwa da su a ranar 13 ga watan Yuni, sun samu ‘yanci.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun sace ɗaliban jami’ar Jos bakwai

“Rundunar ta ɗauki matakin ne nan take bayan da aka samu rahoton lamarin, ta yi aiki tuƙuru tare da haɗin gwiwar sashin yaƙi da garkuwa da mutane da ‘yan uwa da sauran al’umma domin ganin an sako waɗanda lamarin ya shafa.

“An ƙubutar da biyar daga cikin waɗanda aka kashe, ɗaya ya tsere daga kogon masu garkuwa da mutane, yayin da guda ɗaya ke hannun garkuwa,” in ji Alabo.

Ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar Bartholomew Onyeka, ya umarci kwamandan Metro na yankin, da kuma jami’in ‘yan sanda reshen jihar Nasarawa Gwong, da su tabbatar da cewa an ceto wanda ya saura a hanunsu na bakwai ba tare da an ji masa rauni ba, tare kuma da kama waɗanda suka aikata laifin.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya bayar da rahoton cewa, an yi garkuwa da mutanen ne a masauƙinsu da ke kusa da harabar jami’ar a ranar Litinin da daddare a garin Jos a lokacin da suke shirin zana jarrabawar zango na biyu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...