No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugaba Bola Tinubu ya naɗa tsohon shugaban hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa ta EFCC, Nuhu Ribaɗo a matsayin mai ba shi shawara na musamman kan harkokin tsaro da kuma tsohon kwamishinan yaɗa labarai na jihar Legas, Dele Alake a matsayin mai ba shi shawara na musamman kan ayyuka na musamman, sadarwa da dabaru.

Sanarwar da daraktan yaɗa labarai na fadar gwamnatin jihar Abiodun Oladunjoye ya fitar ta kuma ce shugaban ƙasar ya naɗa Ya’u Darazo a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin siyasa da gwamnatoci da kuma Wale Edun a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin kuɗi.

KU KUMA KARANTA: Majalisar Dattawa ta amince da buƙatar Tinubu na naɗa masu ba da shawara na musamman guda 20

A cewar sanarwar, Tinubu ya kuma amince da naɗin Olu Verheijen a matsayin mai ba da shawara na musamman kan makamashi da Zachaeus Adedeji a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin kudaden shiga.

Haka kuma shugaban ƙasar ya amince da su John Ugochukwu Uwajumogu a matsayin mai ba shi shawara na musamman kan harkokin masana’antu, kasuwanci da zuba jari da Dakta Salma Ibrahim Anas a matsayin mai ba da shawara ta musamman kan harkokin kiwon lafiya.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

3 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...