Connect with us

Labarai

Gwamnatin Edo ta ƙara albashi mafi ƙaranci zuwa dubu 40,000, ta rage ranakun aiki zuwa sau uku a mako

Published

on

Gwamnatin jihar Edo ta sanar da cewa ta ƙara albashi mafi ƙaranci daga N30,000 zuwa naira dubu 40,000 duk wata domin rage raɗaɗin tattalin arziƙin da ake samu sakamakon cire tallafin man fetur.

Har ila yau, gwamnatin jihar ta bayyana cewa ta rage yawan kwanakin zuwa aiki daga sau biyar zuwa sau uku a cikin mako guda ga ma’aikatan jihar.

An bayyana hakan ne a wata sanarwa da aka fitar a ranar laraba, 7 ga watan Yuni.

Gwamnan jihar ta baiwa ma’aikata tabbacin cewa jihar za ta tallafa musu ta kowace hanya domin rage raɗaɗin tattalin arziƙi da cire tallafin da ake samu.

KU KUMA KARANTA: Ya kamata a duba batun ‘mafi ƙarancin albashi’, Tinubu ya gayawa gwamnonin APC

“Bayan cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi, farashin man fetur ya ƙaru a ƙasar wanda ya kai ga tashin farashin kayayyaki da ayyuka da kuma tsadar rayuwa baki ɗaya,” in ji ta.

“A matsayinmu na gwamnati mai fafutuka, tun daga nan muka ɗauki matakin ƙara mafi ƙarancin albashin ma’aikata a jihar Edo daga dubu 30,000 da aka amince da shi zuwa dubu 40,000, wanda shi ne mafi girma a ƙasar a yau.

“Muna so mu tabbatar muku da cewa za mu ci gaba da biyan wannan kuɗi, yayin da muke fatan ƙara yawan kuɗaɗen da za a samu idan aka samu ƙarin kaso daga gwamnatin tarayya a jihar mu bisa la’akari da tanadin da ake sa ran za a samu ta hanyar cire tallafin man fetur.

“Mun san wahalhalun da wannan manufa ta haifar wanda ya ƙara tsadar sufuri, tare da cin buri a cikin albashin ma’aikata a jihar.

“Saboda haka, gwamnatin jihar Edo za ta rage yawan kwanakin aiki da ma’aikatan gwamnati da na gwamnati za su riƙa zuwa wuraren ayyukansu daga kwana biyar a mako zuwa kwana uku a mako har sai an sanar da su.

Ma’aikata yanzu za su yi aiki daga gida kwana biyu a kowane mako, “in ji sanarwar.

Obaseki ya ƙara da cewa, jihar na kuma ƙoƙarin samar da ƙarin azuzuwan karatu, ta yadda za a rage tsadar zirga-zirgar iyaye da malamai da ɗalibai zuwa makaranta.

“Hukumar Edo SUBEB za ta bayar da cikakkun bayanai kan wannan shiri a cikin kwanaki masu zuwa.

Domin rage tsadar wutar lantarki ga jama’armu, za mu ci gaba da haɗa kai da kamfanonin wutar lantarki a jihar domin inganta samar da wutar lantarki ga gidaje da kasuwanci.

“Hakazalika, ana samar da hanyoyin haɗin ‘fiber optic’ don taimakawa mutanenmu suyi aiki daga nesa, ta yadda za su rage farashin sufuri.”

A baya jaridar Neptune Prime ta bayar da rahoton cewa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da dakatar da tallafin man fetur bayan da gwamnatin da ta shuɗe kawai ta yi tanadin tallafin har zuwa ƙarshen watan Yuni.

Sanarwar ta haifar da tashin gwauron zabin farashin man fetur daga manyan ‘yan kasuwar man da suka haɗa da Kamfanin Mai na Najeriya (NNPC) Limited.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like