Connect with us

Labarai

Ɓarayi sun kai hari gidan yaɗa labarai, sun sace kayayyakin aiki a gidan rediyon Kogi

Published

on

Wasu da ake kyautata zaton ɓarayi ne sun lalata kayan watsa labarai da wasu kayayyaki masu daraja a gidan rediyon jihar Kogi, da ke Ochaja.

An tattaro cewa an kai wa gidan rediyon jihar da ke Ochaja hari a daren ranar Litinin yayin da ɓarayin suka yi awon gaba da kayan watsa labarai da dama, haɗi da wasu kayayyaki masu daraja.

Jami’an ma’aikatar ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan Yaɗa Labarai da Sadarwa, Mista Kingsley Fanwo da babban darakta na Hukumar Yaɗa Labarai ta Jihar Kogi, Alhaji. Ojo Oyila Ozovehe, ya kai ziyarar tantancewar kai tsaye gidan rediyon domin sanin irin ɓarnar da aka yi a tashar.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan bindiga sun kai hari kan tawagar motocin gwamnan Kogi Yahaya Bello, da yawa sun jikkata

Sai dai Gwamna Alhaji Yahaya Bello ya umurci jami’an tsaro da su tabbatar da an kama waɗanda suka aikata laifin tare da gurfanar da su a gaban ƙuliya domin daƙile aukuwar hakan nan gaba.

Kwamishinan ‘yan sandan, Mista Kingsley Fanwo a cikin wata sanarwa da ya fitar ya ce hukumomin tsaro na samun bayanan sirri masu amfani da za su taimaka wajen gudanar da bincike a yayin da ofishin ‘yan sanda na Egume ke aiki ba dare ba rana domin kamo waɗanda suka aikata laifin.

“Tare da irin ɓarnar da aka yi a tashar, abin takaici ne a lura da cewa Hukumar Kula da Watsa Labarai ba za ta iya yin aiki ba har yanzu.

Sai dai gwamnati ta duƙufa wajen maido da tashar ta iska da wuri “Yayin da muke gode wa Uban masarautar al’ummar da suka karɓi baƙuncinsa saboda damuwarsa kan wannan mummunan lamari.

Muna ƙira ga al’ummomin da ke da kayayyakin more rayuwa na gwamnati da su tabbatar da tsaron ababen more rayuwa saboda ɓarnar irin waɗannan kadarorin na rage saurin ci gaba.

1 Comment

1 Comment

  1. Pingback: Harin ƙunar baƙin wake a Somaliya ya kashe sojoji 13 | Neptune Prime Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like