No menu items!

Sample Page Title

Date:

Majalisar dattawa ta amince da buƙatar shugaban ƙasa Bola Tinubu na naɗa mashawarta na musamman guda 20.

Buƙatar shugaba Tinubu na ƙunshe ne a cikin wata wasiƙa da shugaban majalisar dattawa Ahmad Lawan ya karanta a zauren taron ranar Talata.

Bayan karanta wasiƙar, shugaban majalisar dattawa, Ibrahim Gobir, APC – Sokoto East, ya ce “Majalisar ta yi la’akari da buƙatar.

Shugaban marasa rinjaye na majalisar dattijai, Philip Aduda ne ya goyi bayan ƙudirin, bayan nan ne majalisar ta amince da shi.

KU KUMA KARANTA: Majalisar dokokin Kano ta amince da dokar kare haƙƙin yara

Sai dai shugaban bai sanya sunayen masu ba da shawara ga wasiƙar da Lawan ya karanta ba.

Wannan shi ne karon farko da Tinubu ya buƙaci da a amince masa ya naɗa muƙamin siyasa a Majalisar ƙasar tun bayan rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...