No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya naɗa Abdulƙadir Abdussalam a matsayin sabon Akanta Janar na jihar.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Dawakin-Tofa ya fitar ranar Alhamis.

Ya ce Gwamnan ya kuma naɗa Garba Ahmed-Bichi a matsayin sabon Manajan Daraktan Hukumar Ruwa ta Jihar Kano.

Gwamna Abba, a cewar sanarwar, ya kuma naɗa Rahila Mukhtar a matsayin Babbar Sakatariyar Hukumar Kula da Gudumawar Kiwon Lafiya ta Jihar Kano, (KCHMA).

KU KUMA KARANTA: Sabon Gwamnan Kano Abba Gida-Gida, ya naɗa shugaban ma’aikata da sakataren gwamnati

Sanarwar ta ci gaba da cewa gwamnan ya kuma amince da naɗin Hassan Baba-Danbaffa a matsayin Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tituna ta Jihar Kano, (KARMA).

Gwamnan ya kuma naɗa Ibrahim Yakubu, Manajan Darakta na Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano, (KNUPDA).

Dawakin-Tofa ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba za a sanar da bikin rantsar da waɗanda aka naɗa domin samun damar karɓar ragamar mulki nan take.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...