No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar fansho ta ƙasa, PenCom, a ranar Laraba, ta nesanta kanta da wata jarida mai cike da ƙarya, tana zargin ta fara ɗaukar ma’aikata a shekarar 2023/2024.

Abdulqadir Ɗahiru a wata sanarwa da ya fitar a Legas, ya ce hukumar ba ta da alaƙa da adireshin gidan yanar gizon: www.recruitmentfile.net da wasu ‘yan damfara suka samar, don cutar jama’a.

“Baddar ta bayyana cewa waɗanda suka cancanta su gabatar da aikace-aikacensu ta hanyar tashar ɗaukar ma’aikata a gidan yanar gizon hukumar.

“An yi ƙira ga jama’a da su lura cewa labarin ƙarya ne kuma babu wani ɗaukan aikin da ake yi.

KU KUMA KARANTA: Ayi hattara da ‘hukumar EFCC na bogi’ – EFCC

“A halin yanzu dai hukumar ta kai rahoton shafin yanar gizon ga hukumomin da abin ya shafa domin ɗaukar matakin da ya dace.”

Ɗahiru ya ce duk sahihin bayanai game da ayyukan hukumar ana samun su a gidan yanar gizon ta: www.pencom.gov.ng da kuma hanyoyin sadarwar ta: Facebook: @PenCom.gov, da Twitter: @PenComNig.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...