No menu items!

Sample Page Title

Date:

Sabon gwamnan jihar Zamfara da aka rantsar, Dauda Lawal Dare, ya zargi tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle, da barin asusun jihar da basussuka masu ɗimbin yawa.

Lawal ya bayyana hakan ne jim kaɗan bayan an rantsar da shi a matsayin gwamnan jihar a ranar Litinin.

Gwamnan, ya yi alƙawarin kawo ci gaba cikin sauri tare da magance ɗimbin ƙalubalen da ke fuskantar jihar.

“Ina so in sanar da jama’ar jihar cewa, asusun jihar babu ko kwabo, ya bar jihar da ɗimbin basussuka da suka kai biliyoyin nairori.

“Saboda haka, ina ƙira ga al’ummar jihar da su ƙara haƙuri tare da ba ni cikakken goyon baya da haɗin kai a wannan lokaci mai wahala.

KU KUMA KARANTA: An rantsar da Zulum, ya godewa al’ummar jihar Borno da suka sake zaɓensa a karo na biyu

“Na yi alƙawarin kawo ci gaba cikin sauri a jihar a lokacin yaƙin neman zaɓe, musamman ta fuskar tsaro, ilimi, samar da ayyukan yi, lafiya da kuma noma,” inji shi.

Lawal, wanda ya ce ya zo ne domin ceto jihar Zamfara, ya kuma yi ƙira ga matasa da su guji duk wani nau’i na miyagun ayyuka.

“Na zo ne domin ceto jihar Zamfara da yardar Allah kuma zan yi iya ƙoƙarina wajen ciyar da jihar gaba,” in ji gwamnan.

Tfohon gwamnan Matawalle da mataimakinsa Hassan Nasiha ba su halarci bikin rantsarwar ba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...