No menu items!

Sample Page Title

Date:

Aƙalla ’yan ƙasar Filifin (Philippines) miliyan 73 ne ke fama da ciwon haƙori, abin da ya sa cutar ta zama “mummunan damuwar kiwon lafiya” a ƙasar kudu maso gabashin Asiya, in ji Ma’aikatar Lafiya ta Philippines, DOH, a ranar Laraba.

“Cutar hakori annoba ce ta shiru,” in ji Manuel Vallesteros, babban jami’in sashen kula da rigakafin cututtuka na DOH, ya bayyana hakan bayan wani taron kwamitin a majalisar wakilai.

KU KUMA KARANTA: Sama da mutane miliyan ɗaya sun rasa muhallansu a Somaliya – Hukumomin agaji

Vallesteros ya ce bayanan DOH sun dogara ne akan binciken lafiya na ƙasa na 2018, tare da lura cewa adadin yanzu ya fi girma idan aka kwatanta da lokacin da cutar ta COVID-19 ta hana samun sabis na haƙori sama da shekaru biyu.

Ya lura cewa takwas daga cikin 10 na Filipinas suna fama da “caries na yara” ko “ruɓewar haƙoran jarirai” saboda ana ciyar da su da kayan abinci mai zaƙi.

“Halin lafiyar baki na yaran Filipin yana da ban tsoro,” in ji DOH, ta ƙara da cewa cutar baki “ya ci gaba da zama babbar matsalar lafiyar jama’a” a Philippines.

A cewar Hukumar Lafiya ta Duniya, (WHO), ciwon haƙori babbar matsala ce ta lafiyar jama’a a duniya kuma cuta ce da ta fi yaɗuwa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...