No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tuni dai yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta a Sudan da ta fara aiki a ranar Alhamis ta lalace, inda aka kai hare-hare ta sama da kuma luguden wuta a kusa da fadar shugaban ƙasa da ke babban birnin kasar Khartoum da safen Alhamis, a cewar Al-Jazeera.

An kuma ji ƙarar harbe-harbe a garin Omdurman da ke maƙwabtaka da shi, kamar yadda shaidun gani da ido suka bayyana a shafin Twitter.

Yarjejeniyar tsagaita buɗe wuta na mako guda da ɓangarorin biyu a rikicin Sudan suka amince da ita ya kamata ta fara aiki daga ranar Alhamis har zuwa ranar 11 ga watan Mayu.

KU KUMA KARANTA: Ɓangarorin da ke gaba da juna a Sudan sun amince da tsagaita buɗe wuta

Sai dai ana ganin damar da za ta iya kasancewa ta yi kaɗan. Tun lokacin da aka fara faɗa a Sudan tsakanin ɓangarorin soji masu biyayya ga manyan janar-janar biyu kusan makonni uku da suka gabata, an sha yin shawarwarin tsagaita buɗe wuta na tsawon sa’o’i 72, sai dai an sha karyawa.

Shugaban ƙasar Sudan, Abdel Fattah al-Burhan, ne ke jagorantar sojoji a fafatawa da tsohon mataimakinsa, Mohammed Hamdan Daglo, wanda ke jagorantar rundunar Rapid Support Forces (RSF).

Janar-janar biyu sun taɓa ƙwace iko da Sudan tare a wani juyin mulkin haɗin gwiwa da sojoji suka yi.

Sai dai kuma rashin jituwar da aka yi ta yi kan yadda za a raba madafun iko ya haifar da ɗa mai ido a tsakanin sansanonin biyu, wanda ya kai ga faɗa a fili a ranar 15 ga Afrilu, ya kuma jefa ƙasar da mazaunanta kusan miliyan 46 cikin wani mummunan rikici.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...