Labarai
Shugaban ƙasa mai jiran gado, Tinubu ya dawo gida, ya ce “a shirye nake da aikin da ke gaba”
Zaɓaɓɓen shugaban ƙasa, kuma shugaban ƙasa mai jiran gado, Bola Ahmed Tinubu ya dawo ƙasar ne da yammacin ranar Litinin bayan tafiyar kimanin wata guda a birnin Paris na ƙasar Faransa.
Ya samu tarba daga ɗimbin abokan arziƙi da magoya bayansa da suka yi ɗafifi a filin jirgin saman Nnamdi Azikwe dake Abuja inda jirginsa ya sauka.
Zaɓaɓɓen shugaban ƙasar dai yana tare da uwargidansa, Sanata Remi Tinubu, da ɗansa, Seyi Tinubu. Daga cikin waɗanda suka samu tarba a filin jirgin akwai zaɓaɓɓen mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima, shugaban majalisar wakilai Femi Gbajabiamila da kuma gwamnoni Simon Lalong (Plateau) da Abubakar Sani-Bello (Niger), tsohon gwamnan jihar Borno, Ali Modu Sheriff.
KU KUMA KARANTA: Buhari, Tinubu sun miƙa ta’aziyyar rasuwar matar Aminu Ɗantata
Haka kuma a filin jirgin akwai tsohon shugaban hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa, Malam Nuhu Ribadu, mataimakin shugaban jam’iyyar APC na ƙasa a arewa, Sanata Abubakar Kyari, mataimakin shugaban jam’iyyar na ƙasa ta Kudu Barista Emma Enekwu, da shugabar mata ta ƙasa Dr. Betta Edu.
Akwai kuma Sanata Barau Jibril, Adeola Olamilekan Yahyi, Opeyemi Bamidele, Dayo Adeyeye, Sabi Abdullahi da Adelere Oriolowo da kuma sakataren kwamitin yakin neman zaɓen shugaban ƙasa da aka rushe kwanan nan, Hon. James Faleke, Hon. Babajimi Benson da Mista Bayo Onanuga, Daraktan yada labarai da yaɗa labarai a kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa da aka rusa.
Da yake jawabi ga ɗimbin jama’ar da suka bi shi gida, zaɓaɓɓen shugaban ƙasar ya ce: “Na yi farin ciki da dawowa, na huta, na samu wartsake, kuma a shirye nake don aikin da ke gaba.
“Ka manta da abin da jita-jita ta faɗa maka, na da ƙarfi, da ƙarfi.” Da aka tambaye shi game da tsare-tsaren sa ga ƙasar, ya ce ya sha tuntuɓa da tsare-tsare da nufin haɗa ƙwaƙƙwarar tawaga ta yadda zai iya taka rawa da zarar ya ɗare karagar mulki a ranar 29 ga watan Mayu.
Zaɓaɓɓen shugaban ƙasar ya bar ƙasar ne a ranar 21 ga watan Maris zuwa birnin Paris domin hutu bayan yaƙin neman zaɓe da kuma lokacin zaɓe.
Al'ajabi
Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas
Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas
Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.
Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.
An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.
KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja
Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.
Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.
Labarai
Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja
Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja
Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.
An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.
Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.
An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.
Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.
Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.
Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.
KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja
Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.
Labarai
NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu
NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu
Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.
Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.
A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.
Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .
Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.
KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J
Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.
Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.
A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.
-
Kotu1 year ago
Kotu tayi watsi da ƙarar APC game da zaɓen Abba Gida Gida
-
Labarai9 months ago
Dalilin da ya sa na saka wa matata sasari – Wani magidanci a Potiskum
-
Ƙasashen Waje1 year ago
Ɗaliban Najeriya a Sudan sun nemi a kwaso su daga ƙasar
-
Labarai1 year ago
‘Yan banga sun kama wani mutum da ke yunƙurin sace yarinya a Kano
Pingback: Zaɓaɓɓen shugaban ƙasa, Tinubu ya yi ganawar sirri da Betara | Neptune Prime Hausa
Pingback: Ba zan mayar da wani yanki na Najeriya saniyar ware ba – Tinubu | Neptune Prime Hausa